Home General Dakarun MNJTF sun kashe kwamandan Boko Haram a Tafkin Chadi

Dakarun MNJTF sun kashe kwamandan Boko Haram a Tafkin Chadi

Rundunar hadin gwiwa mai yaƙi da Boko Haram a Tafkin Chadi MNJTF ta ce ta yi nasarar kashe kwamandan ƙungiyar da mayaƙansa biyar.

Wata sanarwa da rundunar ta fitar ranar Laraba ta ce dakarunta sun fafata da mayaƙan ne a yankin Koulfoua bayan kai musu hari, inda suka kashe kwamandan mai suna Amir Dumkei da wasu ‘yanbindiga biyar.

“‘Yanta’addan ne suka fara kawo hari da farar safiyar Talata a sansanin sojan MNJTF da ke Koulfoua, amma kuma sai suka hadu da ruwan wutar da ya fi ƙarfinsu,” a cewar sanarwar da Kanal Olaniyi Osoba ya fitar.

Ta ƙara da cewa ta ƙwace makamai da dama a hannunsu da suka haɗa da bindiga ƙirar AK-47 tara, da ƙananan jiragen ruwa uku, da ƙunshin harsasai mai girma.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp