Home Labarai Yadda Hukumar KAROTA ta karbi koken direbobin mota a jihar Kano

Yadda Hukumar KAROTA ta karbi koken direbobin mota a jihar Kano

Wasu daga cikin Direbobin Bus a Jihar Kano sun koka bisa yadda Jami’an Hukumar Karota ke matsa mutsu Jahar.

Wannan na cikin wata sanarwa da Mai Magana da yawun hukumar ta KAROTA Abubakar Ibrahim Sharada ya fitar ya kuma aikewa manema labarai a jihar Kano.

Direbobin sun kai Koken ne a shalkwatar Hukumar ta lura da zirga-zirgar ababawan ta jihar Kano da nufin a duba domin magance masu matsalar.

Jagoran ayarin Kungiyar Matasan Direbobi ta Garin Kunya dake yankin Karamar Hukumar Minjibir, Mumfadalu Bukar Sakatare Ya koka bisa yadda jami’an Hukumar Karota Ke yawan kama Motocin Bus a duk lokacin da suka fito don gudanar da sana’ar su.

“Duk da cewar yanzu Direbobin a Daidaita Sahu sun Kwace mana akasarin Fasinjojin da mu direbobin Bus muke dauka hakan bata sanya Jami’an Karota sun saurara mana ba wajen kame Motocin mu”, inji Mumfadalu Sakatare.

“Tun da gwamatin Jahar Kano mai ci yanzu ta dagawa Direbobin A Daidaita Sahu kafa, to muma Direbobin Bus mun cancanci wani karamci na Gwamnati wajen karbar Kudaden shiga.” a cewar Jagoran Direbobin na Matasan Kunya.

Yana magane kan Kudaden Sticker wanda ya ce akan haka Jami’an Hukumar KAROTA Ke yawan kame motocin su.

A jawabin sa, Shugaban Hukumar KAROTA, Hon Faisal Mahmud Kabir ya yabawa Kungiyar Matasan Direbobi ta Garin Kunya bisa Kawo wannan koke da suka yi, a madadin sauran Direbobin Bus.

Manajan Daraktan wanda Daraktan kula da harkokin Kudaden shiga na Hukumar KAROTA, Alh Nura Ahmad Diso Ya wakilta yace abinda direbobin suka kawo koke akan sa hurumi ne na Gwamnatin Tarayya, don haka ya shawar ce su dasu miƙa Koken zuwa Hukumar tattara Kudaden Haraji ta Jahar Kano don magan ce al’amarin.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp