Home General EFCC ta ba da belin tsohon gwamnan Sokoto Tambuwal da ta tsare

EFCC ta ba da belin tsohon gwamnan Sokoto Tambuwal da ta tsare

Hukumar da ke yaki da yi wa masu yi wa tattalin arzikin ƙasa zagon ƙasa a Najeriya EFCC ta bayar da belin tsohon gwamnan jihar Sokoto, Aminu Tambuwal, bayan ta yi masa tambayoyi kan wawushe dukiyar ƙasa da ya kai sama da Naira biliyan 189.

An gayyaci Tambuwal wanda ya mulki jihar Sokoto daga shekarar 2015 zuwa 2023, zuwa hedikwatar EFCC da ke Abuja ranar Litinin, inda ya isa da misalin karfe 11:30 na safe.

Masu bincike sun yi masa tambayoyi kuma daga baya aka tsare shi a shelkwatar hukumar.

Majajiyoyi sun ce, a ranar Talata, aka saki tsohon gwamnan bayan cika sharuddan belinsa, waɗanda aka bayyana a matsayin mara tsauri.

Ƴan adawa sun bayyana tsare tsohon gwamnan da EFCC ta yi, a matsayin wani yunƙuri na karya lagon ƴan adawa da gwamnati maici a ƙasar ke yi.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp