Home DUNIYA Majalisar Dokokin Kano ta Dakatar da Ciyaman din Rano

Majalisar Dokokin Kano ta Dakatar da Ciyaman din Rano

Majalisar jihar Kano
Majalisar jihar Kano

Majalisar dokokin jihar Kano ta dakatar da shugaban karamar hukumar Rano Alhaji Naziru Ya’u na tsawon watanni uku sakamakon rashin Iya tafiyar da mulki da karya dokokin aiki tare da umartar sa ya mika aiki ga mataimakin sa.

Majalisar ta dauki wannan matakin ne yayin zaman da ta gudanar a Wannan Rana ta Laraba.

Rahotanni dai sun nuna cewa ana zargin Shugaban karamar hukumar da aka dakatar da sayar da takin zamani ko karkatar da shi wanda gwamnan jihar Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya rabawa kananan hukumomin kano a watan Yulin da ya gabata.

Ko wacce karamar hukuma ta samu tirela uku na takin zamanin mai dauke da buhu 600 ko wacce mota

Haka kuma Majalisar ta yi karatu na daya akan kudirin dokar kwarya kwaryar kasafin kudi na wannan shekarar da gwamna Abba Kabir Yusuf ya aike mata wanda yakai fiye da naira biliyan dari da sittin da tara.

Akawun majalisar Alhaji Bashir Idris Diso shine yayi karatun a yayin zaman majalissar na yau laraba.

Zaman majalissar Wanda shugaban ta Alhaji Jibril Isma’il Falgore ya jagoranta ya amince Gwamna Abba Kabir Yusuf ya nada Alhaji Sa’id Yahaya a matsayin shugaban hukumar karbar korafi da hana cin hanci da rashawa ta jihar Kano.

Hakan ya biyo bayan rahoton da shugaban kwamitin karbar kirafi na majalissar kuma dan Majalissa mai wakiltar karamar hukumar Dala Alhaji Lawan Hussaini Chediyar Yan Gurasa ya gabatar.

Ya ce Alhaji Sa’id Yahaya ya cika dukkanin Ka’idojin da doka ta tanadar kafin nada mutum a matsayin shugaban hukumar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp