Ina nan daram a Jam’iyyar NNPP – Kwankwaso

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar NNPP a zaben 2023, Rabiu Musa Kwankwaso, ya karyata jita-jitar cewa yana shirin komawa APC ko shiga sabuwar kawance a jam’iyyar ADC.

Kwankwaso ya bayyana haka ne a taron kwamitin zartarwa na jam’iyyar na kasa yau, inda ya ce zai ci gaba da kasancewa a cikin NNPP.

Jam’iyyar ta shiga rikicin shugabanci tun bayan babban taron da wani bangare ya gudanar a Fabrairu, wanda ya janyo rabuwar kawuna tsakanin magoya bayan Kwankwaso da kuma wasu daga cikin mambobin da suke ikirarin kafa jam’iyyar.

A kwanakin baya, bangaren Agbo Major ya bukaci INEC ta dage zabuka kan rikicin tambarin jam’iyyar.

Kwankwaso ya ce jam’iyyar za ta sanar da matakinta a lokacin da ya dace.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com