Home AFIRKA Shugabannin sojin Afrika sun kammala taron tsaro a Abuja

Shugabannin sojin Afrika sun kammala taron tsaro a Abuja

Shugabannin sojin Afrika sun kammala wani taro na ƙoli a Abuja wanda ya mayar da hankali kan yawaitar matsalolin tsaro a nahiyar.

Shugabannin tsaro daga ƙasashe irin su Nijar da Somaliya da Ghana da Masar sun hallara a babban birnin Najeriya domin tattaunawa kan dabarun zaman lafiya da tsaro na cikin gida.

An kammala wannan taro mai tsawon kwanaki uku a ranar Laraba.

Mataimakin shugaban Najeriya, Kashim Shettima ne ya yi jawabi ga mahalarta a lokacin buɗe taron, inda ya buƙaci kasashen Afrika su zama masu fito da sabbin fasahohi a fannin tsaro, tare da gargadin cewa dogaro da hanyoyin waje ba zai dore ba.

Haka kuma, ya jaddada buƙatar ƙara zuba jari a tsaron shafukan sada zumunta da na intanet, ganin yadda barazanar da ba a gani da kuma ta zamani ke karuwa.

Nahiyar na ci gaba da fuskantar matsaloli kamar ta’addanci da laifukan ƙungiyoyi da fashi da makami da hare-hare ƴan bindiga da tasirin sauyin yanayi.

Kungiyar Tarayyar Afrika da ECOWAS sun dage wajen karfafa hadin gwiwar soja, amma hakan ya ci tura sakamakon ƙarancin kuɗaɗe da matsalolin kayan aiki da sabanin siyasa.

Daya daga cikin muhimman batutuwa a taron shi ne kafa Rundunar Tsaron ko-ta-kwana ta Afrika wadda aka daɗe ana shirin kafa ta domin amsa kiran gaggawa, amma aiwatar da ita ya tsaya sakamakon matsaloli wajen dabaru da ƙa’idoji da kuɗade.

Mahalarta sun amince cewa Afrika dole ta samar da sabon tsarin tsaro – wanda ‘yan Afrika za su jagoranta kuma su tsara shi domin magance matsalolin nahiyar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp