Home General Gwamnatin Najeriya ta yi maraba da ɗaure Simon Ekpa a Finland

Gwamnatin Najeriya ta yi maraba da ɗaure Simon Ekpa a Finland

Gwamnatin Najeriya ta yaba da hukuncin da kotun lardin Päijät-Häme da ke ƙasar Finland ta yanke a ranar Litinin, inda ta yanke wa mai fafutikar kafa ƙasar Biyafara Simon Ekpa hukuncin zaman gidan kaso na shekara shida bisa samunsa da laifin ta’addanci.

A wata sanarwa da ministan watsa labarai Mohammed Idris ya fitar, ya ce suna maraba da hukuncin, kuma suna jinjina wa ƙasar ta Finland.

“Hukuncin ya zo a daidai, domin zai zama adalci ga ɗimbin ƴan Najeriya da suka rasa rayukansu da waɗanda suka shiga tashin hankalin a sanaiyar bala’in da su Ekpa suka jefa su,” kamar yadda sanarwar ta bayyana, inda ministan ya ƙara da cewa wannan hukuncin zai ƙara ƙarfafa alaƙar da ke tsakanin Najeriya da Finland.

Sanarwar ta ce Ekpa ya yi shekaru yana tunzura jama’a suna aikata laifuka, wanda ke “ruguza rayuwar iyalai da karya kasuwancin su da mayar da yara marayu da jefa garuruwa da dama cikin fargaba, da ma zama silar mutuwar ɗaruruwan mutane da sunan fafutikar da ke barazana ga haɗin kan Najeriya da ƴancinta.”

Ya ƙara da cewa a shirye gwamnatin Tinubu take ta tsayawa da ƙarfinta wajen kare ƴancin ƙasar da mutuncin ƴan ƙasar baki ɗaya ta hanyar “amfani da diflomasiyyar ƙasa da ƙasa da jami’an tsaro da ɓangaren shari’a domin tabbatar da zaman lafiya da haɗin ƙasar.”

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp