Home General Atiku ya nemi a soke sakamakon zaɓen ƙananan hukumomin Rivers

Atiku ya nemi a soke sakamakon zaɓen ƙananan hukumomin Rivers

Tsohon ɗan takarar shugaban Najeriya a zaɓen 2023, Atiku Abubakar ya yi kira da a soke sakamakon zaɓen ƙananan hukumomi da aka gudanar a jihar Rivers inda ya bayyana zaɓen a matsayin “abin kunya da cin fuskar tsarin dimokraɗiyya”.

Wannan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da Atiku ya fitar a shafinsa na X ranar Lahadi.

Atiku ya ce “Yadda aka gudanar da zaɓen ya nuna cewa jam’iyyar APC tana shirin keta doka don samun nasara ta siyasa.”

“Ina jawo hankalin ‘yan Najeriya da ƙungiyoyin duniya da abokan hulɗa kan yadda gwamnatin Tinubu ke ƙoƙarin karkatar da Najeriya zuwa turba mai haɗari,” in ji shi

Atiku ya buƙaci duk jam’iyyun adawa a jihar Rivers su ƙi amincewa da sakamakon zaɓen, saboda “gwamnatin ba ta da hurumin gudanar da zaɓen.”

Hukumar zaɓe mai zaman kanta ta jihar Rivers (RSIEC) ta ce sakamakon zaɓen ƙananan hukumomin jihar da aka gudanar ranar Asabar ɗin da ta gabata ya nuna cewa jam’iyyar APC ta lashe ƙananan hukumomi 20 daga cikin 23 yayin da PDP ta samu sauran guda uku.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp