Home General Atiku ya nemi a soke sakamakon zaɓen ƙananan hukumomin Rivers

Atiku ya nemi a soke sakamakon zaɓen ƙananan hukumomin Rivers

Tsohon ɗan takarar shugaban Najeriya a zaɓen 2023, Atiku Abubakar ya yi kira da a soke sakamakon zaɓen ƙananan hukumomi da aka gudanar a jihar Rivers inda ya bayyana zaɓen a matsayin “abin kunya da cin fuskar tsarin dimokraɗiyya”.

Wannan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da Atiku ya fitar a shafinsa na X ranar Lahadi.

Atiku ya ce “Yadda aka gudanar da zaɓen ya nuna cewa jam’iyyar APC tana shirin keta doka don samun nasara ta siyasa.”

“Ina jawo hankalin ‘yan Najeriya da ƙungiyoyin duniya da abokan hulɗa kan yadda gwamnatin Tinubu ke ƙoƙarin karkatar da Najeriya zuwa turba mai haɗari,” in ji shi

Atiku ya buƙaci duk jam’iyyun adawa a jihar Rivers su ƙi amincewa da sakamakon zaɓen, saboda “gwamnatin ba ta da hurumin gudanar da zaɓen.”

Hukumar zaɓe mai zaman kanta ta jihar Rivers (RSIEC) ta ce sakamakon zaɓen ƙananan hukumomin jihar da aka gudanar ranar Asabar ɗin da ta gabata ya nuna cewa jam’iyyar APC ta lashe ƙananan hukumomi 20 daga cikin 23 yayin da PDP ta samu sauran guda uku.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp