Home General An yanke wa ɗan Najeriya Simon Ekpa hukuncin ɗaurin shekara 6 a...

An yanke wa ɗan Najeriya Simon Ekpa hukuncin ɗaurin shekara 6 a Finland

Kotu a ƙasar Finland ta yanke wa ɗan Najeriya mai ‘rajin ɓallewar ƙasar Biyafara’, Simon Ekpa hukuncin ɗaurin shekaru shida a gidan yari bisa laifukan ta’addanci.

Kotun ta same shi da laifin ƙoƙarin harzuƙa jama’a da niyyar ta’addanci da kuma shiga cikin ayyukan ƙungiyar ta’addanci.

Kotun ta kuma same shi da laifukan zamba ta haraji da kuma karya doka wanda hakan ya sanya kotun ta yanke masa hukuncin ɗaurin shekara shida a gidan yari.

Kotun ta bayyana cewa Ekpa ya yi ƙoƙarin ƙarfafa rajin ɓallewar yankin Biyafara a kudancin Najeriya ta haramtacciyar hanya tsakanin watan Agustan 2021 zuwa Nuwamban 2024.

Kotun ta ce ya yi amfani da kafafen sada zumunta domin samun shigewa gaba-gaba a wannan fafutika.

Ƙungiyar ƴan-awaren ta kuma samar da wasu ƙungiyoyi masu ɗaukar makami, waɗanda kotun ta bayyana a matsayin na ta’addanci.

A cewar hukuncin, Ekpa ne ya samar wa waɗannan ƙungiyoyin makamai da abubuwa masu fashewa da harsasai ta hanyar wasu mutanensa.

Haka kuma, an same shi da laifin amfani da kafafen sada zumuntarsa wajen ingiza mabiyansa su aikata laifuka a Najeriya.

Kotun ta ce ya dikata duk wadannan laifuka ne ya yin da yake zama a garin Lahti na ƙasar ta Finland, sai dai ya musanta zarge-zargen.

Hukuncin da kotun ta yanke ba shi ba ne na ƙarshe, wanda ake zargin zai iya ɗauka ƙara zuwa kotu ta gaba.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp