Home General Sojoji da DSS sun kashe ƴan bindiga 50 a jihar Neja

Sojoji da DSS sun kashe ƴan bindiga 50 a jihar Neja

Sojojin Najeriya tare da jami’an tsaron farin kaya (DSS) sun kashe aƙalla ƴan bindiga 50 sannan kuma suka kuɓutar da wasu daga cikin mutanen ake garkuwa da su a ƙaramar hukumar Mariga ta jihar Neja.

Jami’an tsaron sun ce sun yi arangama da kusan ƴan bindiga 300 ɗauke makamai a ranar 26 ga Agusta, bayan sun yi ƙoƙarin kai hari a ƙauyen da kuma kai farmaki a sansanin DSS.

“Gaskiya ne, shekaran jiya ne muka samu rahoton fitowar ‘yan bindiga daga jihar Zamfara suna tunkarar yankunanmu daga Katonkoro zuwa Kumbashi har zuwa Gulbin Boka.”

“Amma kafin su isa, mun sanar da jami’an tsaro da muke da su, ciki har da sojoji da ‘yansanda, da DSS, waɗanda suka yi iyakar ƙoƙarinsu wajen tare su domin hana su kai farmaki wuraren da suka saba.”

Amma kuma ya ce ƴan bindigan sun samu hanyar shiga Gulbin Boka inda suka yi garkuwa da mutane da dama.

“Amma a hanyarsu ta komawa Zamfara, mun haɗa hannu da jami’an DSS a Kumbashi, inda muka fatattake su kuma muka kuɓutar da mutanen da aka sace, tare da ƙwato wasu dukiyoyin da suka sace”

Abbas ya tabbatar da cewa ba a samu asarar rai daga ɓangaren mutanen gari ba, amma jami’ai sun hallaka kusan ‘yan bindiga 50 tare da ƙona dukkan baburansu.

“Sai dai kuma an samu hasarar rayuka a cikin jami’anmu.” in ji shi.

Wannan lamari ya biyo bayan kama Abubakar Abba, shugaban kungiyar dabar Mahmuda a yankin Wawa na jihar, wanda DSS ta yi a kwanan nan.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp