Home General Sojoji da DSS sun kashe ƴan bindiga 50 a jihar Neja

Sojoji da DSS sun kashe ƴan bindiga 50 a jihar Neja

Sojojin Najeriya tare da jami’an tsaron farin kaya (DSS) sun kashe aƙalla ƴan bindiga 50 sannan kuma suka kuɓutar da wasu daga cikin mutanen ake garkuwa da su a ƙaramar hukumar Mariga ta jihar Neja.

Jami’an tsaron sun ce sun yi arangama da kusan ƴan bindiga 300 ɗauke makamai a ranar 26 ga Agusta, bayan sun yi ƙoƙarin kai hari a ƙauyen da kuma kai farmaki a sansanin DSS.

“Gaskiya ne, shekaran jiya ne muka samu rahoton fitowar ‘yan bindiga daga jihar Zamfara suna tunkarar yankunanmu daga Katonkoro zuwa Kumbashi har zuwa Gulbin Boka.”

“Amma kafin su isa, mun sanar da jami’an tsaro da muke da su, ciki har da sojoji da ‘yansanda, da DSS, waɗanda suka yi iyakar ƙoƙarinsu wajen tare su domin hana su kai farmaki wuraren da suka saba.”

Amma kuma ya ce ƴan bindigan sun samu hanyar shiga Gulbin Boka inda suka yi garkuwa da mutane da dama.

“Amma a hanyarsu ta komawa Zamfara, mun haɗa hannu da jami’an DSS a Kumbashi, inda muka fatattake su kuma muka kuɓutar da mutanen da aka sace, tare da ƙwato wasu dukiyoyin da suka sace”

Abbas ya tabbatar da cewa ba a samu asarar rai daga ɓangaren mutanen gari ba, amma jami’ai sun hallaka kusan ‘yan bindiga 50 tare da ƙona dukkan baburansu.

“Sai dai kuma an samu hasarar rayuka a cikin jami’anmu.” in ji shi.

Wannan lamari ya biyo bayan kama Abubakar Abba, shugaban kungiyar dabar Mahmuda a yankin Wawa na jihar, wanda DSS ta yi a kwanan nan.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp