Home General Atiku ya nemi a soke sakamakon zaɓen ƙananan hukumomin Rivers

Atiku ya nemi a soke sakamakon zaɓen ƙananan hukumomin Rivers

Tsohon ɗan takarar shugaban Najeriya a zaɓen 2023, Atiku Abubakar ya yi kira da a soke sakamakon zaɓen ƙananan hukumomi da aka gudanar a jihar Rivers inda ya bayyana zaɓen a matsayin “abin kunya da cin fuskar tsarin dimokraɗiyya”.

Wannan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da Atiku ya fitar a shafinsa na X ranar Lahadi.

Atiku ya ce “Yadda aka gudanar da zaɓen ya nuna cewa jam’iyyar APC tana shirin keta doka don samun nasara ta siyasa.”

“Ina jawo hankalin ‘yan Najeriya da ƙungiyoyin duniya da abokan hulɗa kan yadda gwamnatin Tinubu ke ƙoƙarin karkatar da Najeriya zuwa turba mai haɗari,” in ji shi

Atiku ya buƙaci duk jam’iyyun adawa a jihar Rivers su ƙi amincewa da sakamakon zaɓen, saboda “gwamnatin ba ta da hurumin gudanar da zaɓen.”

Hukumar zaɓe mai zaman kanta ta jihar Rivers (RSIEC) ta ce sakamakon zaɓen ƙananan hukumomin jihar da aka gudanar ranar Asabar ɗin da ta gabata ya nuna cewa jam’iyyar APC ta lashe ƙananan hukumomi 20 daga cikin 23 yayin da PDP ta samu sauran guda uku.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp