Home AFIRKA Burkina Faso ta amince da dokar haramta neman maza a faɗin ƙasar

Burkina Faso ta amince da dokar haramta neman maza a faɗin ƙasar

Gwamnatin sojin Burkina Faso ta amince da wata doka da ke haramta neman maza ko luwaɗi a fadin ƙasar, wadda ta tanadi hukuncin ɗaurin shekaru 5 a gidan kaso, lamarin da ya sa ta kasance ƙasar Afirka ta baya-bayan nan da ta samar da wannan doka.

Ƙasashe kimanin 30 a nahiyar Afirka sun haramta ɗabi’ar neman maza, amma Burkina Faso ba ta yi hakan ba gabanin ƙwace mulkin da sojoji suka yi shekaru 3 da suka wuce.

Mambobin majalisar dokokin wucin-gadi da sojoji suka kafa guda 71 ne suka amince da ƙudirin dokar, da aka gabatar.

A jawabin da ya gabatar wa al’ummar ƙasar ta kafar talabijin, ministan shari’a na ƙasar, Edasso Rodrigue Bayala ya ce duk wanda aka kama yana aikata neman maza zai gurfana a gaban alƙali, inda ya ƙara da cewa idan kuma ba dan ƙasa ba ne, za a tasa ƙeyarsa zuwa ƙasarsa.

Dokar na daga cikin dokokin da aka bijiro da su a ƙasar da zummar sake fasalin iyali da tsarin zamantakewar ‘yan ƙasa, kuma za a sanar da al’umma wannan doka ta wajen gudanar da gangami a faɗin ƙasar.

Mali, wadda aminiyar Burkina Faso ce, ta yi wannan doka  da ke haramta luwaɗi a watan Nuwamban shekarar 2024.

Ghana da Uganda sun tsaurara dokokinsu da ke yaƙi da ɗabi’ar neman maza a cikin shekarun baya-bayan nan, lamarin da ya janyo caccaka.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp