Home Labarai NUPENG ta cimma matsaya da kamfanin Dangote

NUPENG ta cimma matsaya da kamfanin Dangote

Ƙungiyar ƙwadago ta ma’aikatan dakon man fetur da iskar gas a Najeriya, NUPENG ta dakatar da yajin aikin da ta shirya bayan cimma matsaya da kamfanin Dangote Refinery kan ’yancin mutane na kafa ƙungiya.

Wanne na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da NUPENG ɗin ta fitar a shafinta na X.

Cimma matsayar ya biyo bayan ganawa ta musamman da hukumar DSS ta kira, tare da halartar Ministan Kuɗi, Wale Edun, da shugabannin NLC da TUC.

A cikin yarjejeniyar da aka sanya hannu, an amince cewa ma’aikatan kamfanin da ke son shiga ƙungiya za su samu damar yin hakan, tare da fara tsarin nan take da kuma kammala shi cikin makonni biyu.

a cewar yarjejeniya, babu wani ma’aikacin Dangote da za zalunta saboda sanarwar yajin aikin.

Da wannan matsaya, NUPENG ta dakatar da yajin aikin da ta shirya gudanarwa, yayin da ɓangarorin biyu za su koma wurin Ministan Ƙwadago bayan mako guda domin bayar da rahoto

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp