Ƙungiyar ƙwadago ta Najeriya TUC ta yi watsi da matakin gwamnatin tarayya na ƙara kaso 5% cikin 100% kan farashin kowacce litar mai, tana mai kwatanta hakan a matsayin ganganci da mugunta ga tattalin arzikin ƙasar.
Read Also:
Tuni dai ƙungiyar ta baiwa gwamnatin wa’adin kwanaki 14 da ta janye wannan matakin, ko kuma ta ɗauki matakin da take ganin ya dace.
A cewarta cikin matakin da zata ɗauka har da rufe manyan sassan gwamnati musamman basu samar da kuɗaɗen shiga.
Ta cikin wata sanarwa da Festus Osifo da kuma Nuhu Toro shugabannin ƙungiyar suka sanyawa hannu, sun ce a halin da ake ciki ƴan Najeriya na cikin ƙangin biyan haraje-haraje barkatai.
Shugabannin ƙungiyar ƙwadagon, sun ce sabon harajin ba abu ne da zai yiwu ba, don haka ya zama wajibi gwamnati ta dakatar da shi.
A cewarsu ƙungiyar har yanzu ƴan Najeriya basu gama farfaɗowa daga ƙangin da cire tallafin man fetur ya jefa su, baya ga lalacewar darajar Naira.
Tuni dai ƙungiyar ta ce ta fara sanar da sassanta na jihohi don shirin tafiya yajin aiki, idan hakan ta kama.











