Home General Ƙungiyar ƙwadago ta TUC ta yi barazanar shiga yajin aiki a Najeriya

Ƙungiyar ƙwadago ta TUC ta yi barazanar shiga yajin aiki a Najeriya

Ƙungiyar ƙwadago ta Najeriya TUC ta yi watsi da matakin gwamnatin tarayya na ƙara kaso 5% cikin 100% kan farashin kowacce litar mai, tana mai kwatanta hakan a matsayin ganganci da mugunta ga tattalin arzikin ƙasar.

A cewar gwamnatin tarayyar ta ɗauki wannan mataki ne don samun kuɗaɗen shiga da za’a yi amfani da su wajen gina hanyoyi da sauran manyan ayyuka a ƙasar.

Tuni dai ƙungiyar ta baiwa gwamnatin wa’adin kwanaki 14 da ta janye wannan matakin, ko kuma ta ɗauki matakin da take ganin ya dace.

A cewarta cikin matakin da zata ɗauka har da rufe manyan sassan gwamnati musamman basu samar da kuɗaɗen shiga.

Ta cikin wata sanarwa da Festus Osifo da kuma Nuhu Toro shugabannin ƙungiyar suka sanyawa hannu, sun ce a halin da ake ciki ƴan Najeriya na cikin ƙangin biyan haraje-haraje barkatai.

Shugabannin ƙungiyar ƙwadagon, sun ce sabon harajin ba abu ne da zai yiwu ba, don haka ya zama wajibi gwamnati ta dakatar da shi.

A cewarsu ƙungiyar har yanzu ƴan Najeriya basu gama farfaɗowa daga ƙangin da cire tallafin man fetur ya jefa su, baya ga lalacewar darajar Naira.

Tuni dai ƙungiyar ta ce ta fara sanar da sassanta na jihohi don shirin tafiya yajin aiki, idan hakan ta kama.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp