Home General Ƙungiyar ƙwadago ta TUC ta yi barazanar shiga yajin aiki a Najeriya

Ƙungiyar ƙwadago ta TUC ta yi barazanar shiga yajin aiki a Najeriya

Ƙungiyar ƙwadago ta Najeriya TUC ta yi watsi da matakin gwamnatin tarayya na ƙara kaso 5% cikin 100% kan farashin kowacce litar mai, tana mai kwatanta hakan a matsayin ganganci da mugunta ga tattalin arzikin ƙasar.

A cewar gwamnatin tarayyar ta ɗauki wannan mataki ne don samun kuɗaɗen shiga da za’a yi amfani da su wajen gina hanyoyi da sauran manyan ayyuka a ƙasar.

Tuni dai ƙungiyar ta baiwa gwamnatin wa’adin kwanaki 14 da ta janye wannan matakin, ko kuma ta ɗauki matakin da take ganin ya dace.

A cewarta cikin matakin da zata ɗauka har da rufe manyan sassan gwamnati musamman basu samar da kuɗaɗen shiga.

Ta cikin wata sanarwa da Festus Osifo da kuma Nuhu Toro shugabannin ƙungiyar suka sanyawa hannu, sun ce a halin da ake ciki ƴan Najeriya na cikin ƙangin biyan haraje-haraje barkatai.

Shugabannin ƙungiyar ƙwadagon, sun ce sabon harajin ba abu ne da zai yiwu ba, don haka ya zama wajibi gwamnati ta dakatar da shi.

A cewarsu ƙungiyar har yanzu ƴan Najeriya basu gama farfaɗowa daga ƙangin da cire tallafin man fetur ya jefa su, baya ga lalacewar darajar Naira.

Tuni dai ƙungiyar ta ce ta fara sanar da sassanta na jihohi don shirin tafiya yajin aiki, idan hakan ta kama.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp