Home Labarai NUPENG ta cimma matsaya da kamfanin Dangote

NUPENG ta cimma matsaya da kamfanin Dangote

Ƙungiyar ƙwadago ta ma’aikatan dakon man fetur da iskar gas a Najeriya, NUPENG ta dakatar da yajin aikin da ta shirya bayan cimma matsaya da kamfanin Dangote Refinery kan ’yancin mutane na kafa ƙungiya.

Wanne na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da NUPENG ɗin ta fitar a shafinta na X.

Cimma matsayar ya biyo bayan ganawa ta musamman da hukumar DSS ta kira, tare da halartar Ministan Kuɗi, Wale Edun, da shugabannin NLC da TUC.

A cikin yarjejeniyar da aka sanya hannu, an amince cewa ma’aikatan kamfanin da ke son shiga ƙungiya za su samu damar yin hakan, tare da fara tsarin nan take da kuma kammala shi cikin makonni biyu.

a cewar yarjejeniya, babu wani ma’aikacin Dangote da za zalunta saboda sanarwar yajin aikin.

Da wannan matsaya, NUPENG ta dakatar da yajin aikin da ta shirya gudanarwa, yayin da ɓangarorin biyu za su koma wurin Ministan Ƙwadago bayan mako guda domin bayar da rahoto

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp