Home General Kotu ta yanke wa kwamandan Ansaru hukunci ɗaurin shekaru 15

Kotu ta yanke wa kwamandan Ansaru hukunci ɗaurin shekaru 15

Court

Wata babba kotu a Abuja babban birnin Najeriya ta yanke wa Mahmud Usman, ɗaya daga cikin kwamandojin ƙungiyar Ansaru hukuncin ɗaurin shekaru 15 a gidan yari.

Mutumin wanda hukumar tsaro ta DSS ta gurfanar a ranar Alhamis ya amsa laifin gudanar da harkokin haƙar ma’adinai ba bisa ƙa’ida ba, lamarin da ya ba shi damar mallakar makamai da aikata ayyukan ta’addanci da garkuwa da mutane.

Alƙalin kotun mai shari’a Emeka Nwite, ya bayar da umarnin a ajiye Mahmud Usman a ofishin hukumar DSS har zuwa lokacin da za a kammal shari’a kan sauran zarge-zargen da ake masa guda 31.

A lokacin gabatar da ƙarar, an tuhumi Mahmud Usman da Abubakar Abba da aikata ta’addanci a 2022, ta hanyar kai hari kan barikin soji ta Wawa da ke Ka’inji a ƙaramar hukumar Borgu ta jihar Niger, lamain da ya yi sanadiyar kisan mutane da dama.

Ana zargin su da koyon horo a kan sarrafa makamai da haɗa bama-bamai a sansanonin ƴan ta’ada da dama.

Mai shari’a Nwite ya sanya ranar 21 ga watan Oktoba a matsayin ranar da za a ci gaba da shari’ar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Dangote ya ƙara farashin man feturHukumar Jin dadin alhazan Kano ta sanar da ranar fara jigilar maniyatantaYadda Lakurawa suka kashe masallata a KebbiDSS ta kama jagoran ISWAP da ake nema ruwa a jallo a EdoBa mu taɓa goyon bayan musguna wa Kristoci ba - Gwamnatin NajeriyaGobara ta tashi a babban kasuwar Fika da ke jihar YobeWaye Tunji Disu: Sabon Babban Sifeton 'Yansandan NajeriyaNijar ta amince da kundin ayyukan AES na shekara ta biyuAtiku ya zargi gwamnatin Tinubu da yi wa dimokuraɗiyya zagon ƙasaGwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanci
X whatsapp