Home General Gwamnatin Kano ta bayar da hutun bikin Mauludi

Gwamnatin Kano ta bayar da hutun bikin Mauludi

Gwamnatin Jihar Kano ta bayyana rana, Juma’a, 12 ga Satumba, 2025, wanda ya yi daidai da 19 ga Rabi’ul Awwal, 1447 Ah, a matsayin ranar hutu domin bikin tunawa da ranar haihuwar Annabi Muhammad (SAW).

Wannan dai na cikin wata sanarwa da Kwamishinan Yaɗa Labarai da Harkokin Cikin Gida, Comrade Ibrahim Abdullahi Waiya, ya fitar ranar Alhamis, wadda ta ce gwamnatin jihar ta bukaci ma’aikata, ‘yan kasuwa da al’ummar jihar su gudanar da hutun cikin lumana tare da yin koyi da Annabi (SAW).

Sanarwar ta kuma bukaci jama’a da su yi amfani da wannan lokaci wajen tunani kan darussan hadin kai, juriya da biyayya ga doka.

Bugu da ƙari, gwamnatin ta ja hankalin jama’a da su yi addu’o’i na musamman domin samun zaman lafiya, ci gaba da bunƙasar Kano da Najeriya baki ɗaya.

Gwamnatin jihar ta kuma taya al’ummar Kano murnar wannan rana mai albarka tare da fatan samun bikin Maulud cikin kwanciyar hankali da farin ciki.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp