Home General Gwamnatin Kano ta bayar da hutun bikin Mauludi

Gwamnatin Kano ta bayar da hutun bikin Mauludi

Gwamnatin Jihar Kano ta bayyana rana, Juma’a, 12 ga Satumba, 2025, wanda ya yi daidai da 19 ga Rabi’ul Awwal, 1447 Ah, a matsayin ranar hutu domin bikin tunawa da ranar haihuwar Annabi Muhammad (SAW).

Wannan dai na cikin wata sanarwa da Kwamishinan Yaɗa Labarai da Harkokin Cikin Gida, Comrade Ibrahim Abdullahi Waiya, ya fitar ranar Alhamis, wadda ta ce gwamnatin jihar ta bukaci ma’aikata, ‘yan kasuwa da al’ummar jihar su gudanar da hutun cikin lumana tare da yin koyi da Annabi (SAW).

Sanarwar ta kuma bukaci jama’a da su yi amfani da wannan lokaci wajen tunani kan darussan hadin kai, juriya da biyayya ga doka.

Bugu da ƙari, gwamnatin ta ja hankalin jama’a da su yi addu’o’i na musamman domin samun zaman lafiya, ci gaba da bunƙasar Kano da Najeriya baki ɗaya.

Gwamnatin jihar ta kuma taya al’ummar Kano murnar wannan rana mai albarka tare da fatan samun bikin Maulud cikin kwanciyar hankali da farin ciki.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp