Home General Gwamnatin Kano ta bayar da hutun bikin Mauludi

Gwamnatin Kano ta bayar da hutun bikin Mauludi

Gwamnatin Jihar Kano ta bayyana rana, Juma’a, 12 ga Satumba, 2025, wanda ya yi daidai da 19 ga Rabi’ul Awwal, 1447 Ah, a matsayin ranar hutu domin bikin tunawa da ranar haihuwar Annabi Muhammad (SAW).

Wannan dai na cikin wata sanarwa da Kwamishinan Yaɗa Labarai da Harkokin Cikin Gida, Comrade Ibrahim Abdullahi Waiya, ya fitar ranar Alhamis, wadda ta ce gwamnatin jihar ta bukaci ma’aikata, ‘yan kasuwa da al’ummar jihar su gudanar da hutun cikin lumana tare da yin koyi da Annabi (SAW).

Sanarwar ta kuma bukaci jama’a da su yi amfani da wannan lokaci wajen tunani kan darussan hadin kai, juriya da biyayya ga doka.

Bugu da ƙari, gwamnatin ta ja hankalin jama’a da su yi addu’o’i na musamman domin samun zaman lafiya, ci gaba da bunƙasar Kano da Najeriya baki ɗaya.

Gwamnatin jihar ta kuma taya al’ummar Kano murnar wannan rana mai albarka tare da fatan samun bikin Maulud cikin kwanciyar hankali da farin ciki.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp