Home General Hukumar DSS ta yi holen manyan kwamandojin ƙungiyar Ansaru

Hukumar DSS ta yi holen manyan kwamandojin ƙungiyar Ansaru

Hukumar DSS a Najeriya ta yi holen manyan kwamandojin ƙungiyar Ansaru da ta kama a watan da ya gabata, yayin da ake tuhumarsu da laifukan ta’addanci a babbar kotun tarayya da ke Abuja.

Waɗanda ake zargin sun haɗar da Mahmud Usman wanda aka fi sani da Abu Bara’a sai kuma Mahmud Al-Nigeri, wanda aka fi sani da Malam Mamuda.

Tuni hukumar ta shigar da ƙararraki guda 32 kan mutanen gaban mai shari’a Emeka Nwite.

Tuhumar da ake yiwa mutanen biyu akwai zargin haɗa kai da kuma tsarawa tare da ƙaddamar da hari kan gidan yarin kuje a watan Yulin 2022, wanda ya baiwa ɗaurarru sama da 600 damar tserewa.

Haka kuma sune ake zargi da kai hari kan barikin sojoji na Wawa da ke Kainji da ke jihar Naija, inda aka tafka asarar rayuka da dukiyoyi.

Hukumar ta DSS ta ce rahoton binciken ya nuna yadda waɗannan mayaƙa suka karɓi horo na musamman a sansanonin ƴan ta’adda da ke ƙasashen Mali da kuma Libya kan ƙaddamar da hari, sarrafa makamai da kuma dubarun yaƙi.

Mahmuda kuwa ya karɓi wani horo mai matuƙar haɗari a tsakanin shekarar 2013 zuwa 2015 a hannun wata ƙungiyar ta’addanci ta ƙasa da ƙasa.

DSS ta kuma ce waɗannan mutane biyu sune suka jagoranci manyan hare-haren ta’addanci da garkuwa da mutane ciki har da ɗaya daga cikin injiniyoyin ƙasar Faransa da ke aiki a Najeriya Francis Collomp a shekarar 2013 da kuma Alhaji Musa Umar Uba Magajin Daura a 2019.

Waɗannan mutane ne kuma suka kai hari kan guda daga cikin kamfanonin sarrafa Uranium a jamhuriyar Nijar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp