Home General Hukumar DSS ta yi holen manyan kwamandojin ƙungiyar Ansaru

Hukumar DSS ta yi holen manyan kwamandojin ƙungiyar Ansaru

Hukumar DSS a Najeriya ta yi holen manyan kwamandojin ƙungiyar Ansaru da ta kama a watan da ya gabata, yayin da ake tuhumarsu da laifukan ta’addanci a babbar kotun tarayya da ke Abuja.

Waɗanda ake zargin sun haɗar da Mahmud Usman wanda aka fi sani da Abu Bara’a sai kuma Mahmud Al-Nigeri, wanda aka fi sani da Malam Mamuda.

Tuni hukumar ta shigar da ƙararraki guda 32 kan mutanen gaban mai shari’a Emeka Nwite.

Tuhumar da ake yiwa mutanen biyu akwai zargin haɗa kai da kuma tsarawa tare da ƙaddamar da hari kan gidan yarin kuje a watan Yulin 2022, wanda ya baiwa ɗaurarru sama da 600 damar tserewa.

Haka kuma sune ake zargi da kai hari kan barikin sojoji na Wawa da ke Kainji da ke jihar Naija, inda aka tafka asarar rayuka da dukiyoyi.

Hukumar ta DSS ta ce rahoton binciken ya nuna yadda waɗannan mayaƙa suka karɓi horo na musamman a sansanonin ƴan ta’adda da ke ƙasashen Mali da kuma Libya kan ƙaddamar da hari, sarrafa makamai da kuma dubarun yaƙi.

Mahmuda kuwa ya karɓi wani horo mai matuƙar haɗari a tsakanin shekarar 2013 zuwa 2015 a hannun wata ƙungiyar ta’addanci ta ƙasa da ƙasa.

DSS ta kuma ce waɗannan mutane biyu sune suka jagoranci manyan hare-haren ta’addanci da garkuwa da mutane ciki har da ɗaya daga cikin injiniyoyin ƙasar Faransa da ke aiki a Najeriya Francis Collomp a shekarar 2013 da kuma Alhaji Musa Umar Uba Magajin Daura a 2019.

Waɗannan mutane ne kuma suka kai hari kan guda daga cikin kamfanonin sarrafa Uranium a jamhuriyar Nijar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp