Home General Hukumar DSS ta yi holen manyan kwamandojin ƙungiyar Ansaru

Hukumar DSS ta yi holen manyan kwamandojin ƙungiyar Ansaru

Hukumar DSS a Najeriya ta yi holen manyan kwamandojin ƙungiyar Ansaru da ta kama a watan da ya gabata, yayin da ake tuhumarsu da laifukan ta’addanci a babbar kotun tarayya da ke Abuja.

Waɗanda ake zargin sun haɗar da Mahmud Usman wanda aka fi sani da Abu Bara’a sai kuma Mahmud Al-Nigeri, wanda aka fi sani da Malam Mamuda.

Tuni hukumar ta shigar da ƙararraki guda 32 kan mutanen gaban mai shari’a Emeka Nwite.

Tuhumar da ake yiwa mutanen biyu akwai zargin haɗa kai da kuma tsarawa tare da ƙaddamar da hari kan gidan yarin kuje a watan Yulin 2022, wanda ya baiwa ɗaurarru sama da 600 damar tserewa.

Haka kuma sune ake zargi da kai hari kan barikin sojoji na Wawa da ke Kainji da ke jihar Naija, inda aka tafka asarar rayuka da dukiyoyi.

Hukumar ta DSS ta ce rahoton binciken ya nuna yadda waɗannan mayaƙa suka karɓi horo na musamman a sansanonin ƴan ta’adda da ke ƙasashen Mali da kuma Libya kan ƙaddamar da hari, sarrafa makamai da kuma dubarun yaƙi.

Mahmuda kuwa ya karɓi wani horo mai matuƙar haɗari a tsakanin shekarar 2013 zuwa 2015 a hannun wata ƙungiyar ta’addanci ta ƙasa da ƙasa.

DSS ta kuma ce waɗannan mutane biyu sune suka jagoranci manyan hare-haren ta’addanci da garkuwa da mutane ciki har da ɗaya daga cikin injiniyoyin ƙasar Faransa da ke aiki a Najeriya Francis Collomp a shekarar 2013 da kuma Alhaji Musa Umar Uba Magajin Daura a 2019.

Waɗannan mutane ne kuma suka kai hari kan guda daga cikin kamfanonin sarrafa Uranium a jamhuriyar Nijar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp