Home Labarai Ƴanbindiga sun hallaka mutum 22 a Jamhuriyyar Nijar

Ƴanbindiga sun hallaka mutum 22 a Jamhuriyyar Nijar

Wasu mutane ɗauke da bindigogi a kan babura sun harbe akalla mutum 22 a wani kauye da ke yammacin jamhuriyyar Nijar.

Wani mazaunin ƙauyen ya shaida wa kamfanin dillancin labarai na AFP, cewa yawancin mutanen an kashe su ne a yayin da suke halartar wani biki.

Ƙauyen na yankin Tilaberi ne wanda ke da iyaka da Mali da kuma Burkina Faso.

Shugabannin mulkin sojin ƙasar ya ce gwamnatinsa na ta fadi tashi ganin daƙile ayyukan masu ikirarin jihadi a yankin.

A ranar Talata ne shugaban ƙungiyar ECOWAS ya kai wata ziyara Burkin Faso don neman haɗin kan ƙsasashen da ke ƙungiyar (AES) ciki har da Nijar wajen yaƙi da mahara da masu tayar da ƙayar baya a yankin na Sahel.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp