Wasu mutane ɗauke da bindigogi a kan babura sun harbe akalla mutum 22 a wani kauye da ke yammacin jamhuriyyar Nijar.
Wani mazaunin ƙauyen ya shaida wa kamfanin dillancin labarai na AFP, cewa yawancin mutanen an kashe su ne a yayin da suke halartar wani biki.
Ƙauyen na yankin Tilaberi ne wanda ke da iyaka da Mali da kuma Burkina Faso.
Shugabannin mulkin sojin ƙasar ya ce gwamnatinsa na ta fadi tashi ganin daƙile ayyukan masu ikirarin jihadi a yankin.
A ranar Talata ne shugaban ƙungiyar ECOWAS ya kai wata ziyara Burkin Faso don neman haɗin kan ƙsasashen da ke ƙungiyar (AES) ciki har da Nijar wajen yaƙi da mahara da masu tayar da ƙayar baya a yankin na Sahel.