Home General Sojojin Nijeriya sun hallaka mayakan boko haram 5 a jihohin Borno da...

Sojojin Nijeriya sun hallaka mayakan boko haram 5 a jihohin Borno da Taraba

Dakarun sojin Nijeriya na ci gaba da samun nasarar a yakin da suke na kawar da matsalar rashin tsaro da ya addabi yankin arewa maso gabashi da arewa ta tsakiyar Kasar.

Wannan dai na zuwa ne bayan da sojojin suka sami nasarar hallaka ‘yan ta’adda biyar a mabambanta hare-hare da suka kai a jihohin Borno da Taraba kamar yadda PRNigeria ta sami bayani.

A jihar Borno dake Arewa maso dakarun tsaro na Operation HADIN KAI, bisa hadin gwiwa jami’an CJTF da mafarauta sun kai kai har hai kan mayakan boko haram a yankin Umbo Gen ranar a yammacin litinin a sumame karkashin OperationDesert Sanity IV.

Wata majiya ta shaidawa mai sharhi kan harkokin tsaro a yankin tafkin Chadi Zagazola cewa, dakarun sun afkawa mayakan boko haram a wani bata kasha da suka yi musayara wuta, abin da ya sanya suka sami nasarar hallaka 3 daga cikin su, yayin da wasu kuma suka guda da raunikan harbi a jukkunansu.

Sojojin sun sami nasarar kwato kayayyakin da dama da suka hadar da bindiga kirar AK47 da wayar hannun samfurin Itel, sai dai kuma kawo yanzu rundunar sojin kasar bata bayyana ko ta yi asarar rayukan sojojin ba.

A wani hari makamancin wannan dakarun runduna ta 6 karkashin shiyya ta 3 na dakarun Operation Whirl Stroke (OPWS) sun sami nasarar hallaka mayaka 2 a karamar hukumar takum dake jihar Taraba a wannan rana.

A wani atisaye, da dakarun suka gudanar bayan samun wasu sahihan bayanan sirri, dake cewa ýan ta’addan dake karkashin dabar Bojo, na shirin kai hari kauyen Chanchanji, wannan ne ya sanya dakaru tare su a hanyar Demeva zuwa chanchanji.

Arba tsakanin sojojin da ‘yan ta’addan ta sanya guda cikin ‘yan ta’addan ya mutu, yain da kuma wasu suka mutu a wata arba da aka sake yi a mashigar Demeva zuwa Gbudu.

Dakrun sojojin sun sami nasarar kwato bindiga kirara G3, da alburushi mai tsayin mita 7.62, babur mia kafa biyu. Sojojin kuma sun cigaba da sintiri a yankin domin tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyin al’ummar dake rayuwa a yankin.

Haka kuma sojojin sun tabbatar da dawowar zaman lafiya a yankunan Borno da Taraba da lamarin ya auku bisa cigaba da sintirin da dakarun sojojin ke yi.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp