Home General NDLEA ta kama Ba’indiye da wasu mutane da ƙwaya ta naira biliyan...

NDLEA ta kama Ba’indiye da wasu mutane da ƙwaya ta naira biliyan uku a Legas

Hukumar hana sha da fataucin miyagun kwayoyi ta NDLEA, ta ce ta kama wani ɗan kasar Indiya da wasu mutum uku bisa zarginsu da hannu wajen shigar da ƙwayoyin Tramadol na fiye da naira bilyan uku zuwa cikin kasar.

Hukumar ta NDLEA ta bayyana cewa wannan kamen kwaya shine mafi girma a cikin wannan shekarar da hukumar ta yi, lamarin da ke nuna ƙaruwar safarar muggan ƙwayoyi da ta’ammali da su a Najeriya.

Cikin wata sanarwa da hukumar ta NDLEA ta fitar ta ce jami’anta sun yi nasarar kama mutunan ne a filin jirgin sama na Murtala Muhammad da ke Legas, sakamakon bin kwakkwafi da bayanan sirri da jami’ansu suka samu.

Hukumar ta ce jami’anta sun gano ƙwayoyin tramol din wadanda aka shigo da su a matsayin magani na multivitamins a cikin wasu walaye, ana ƙoƙari fita da su cikin wasu manyan motoci daga filin girjin.

Rahotanni sun nuna cewa likitoci kan bayar da ƙwayar Tramadol ne don rage radadin ciwo, amma a yanzu tana neman zama wata annoba a tsakanin matasa inda ta ke haddasa mummunan maye.

Bayanai na cewa yawan masu amfani da wannan magani a kasashen Afirka da dama na ƙaruwa duk da illar da take yi lamarin da ke tayar da hankali.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp