Home Labarai Gwamnatin Kano ta yi gargaɗi kan zazzaɓi mai tsanani da ke sa...

Gwamnatin Kano ta yi gargaɗi kan zazzaɓi mai tsanani da ke sa mutum zubar da jini

Hukumar kula da cututtuka ta jihar Kano KNCDC ta fitar da sanarwar gargadi ga ƴan jihar dangane da rahoton da hukumar kula da cututtuka ta ƙasa (NCDC) ta bayar kan wasu mutane biyu da ake zargin suna ɗauke da cutar zazzaɓi mai tsanani da ke sa mutum zubar da jini a Abuja.

Wannan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da hukumar ta fitar a shafukan sada zumuntarta. Inda ta ce gargaɗi na daga cikin shirin kare lafiyar al’umma, duba da yadda Kano ke da yawan jama’a da kuma hulɗar kasuwanci da tafiye-tafiye zuwa sauran sassan ƙasar.

Sanarwar ta tabbatar da cewa binciken farko ya nuna waɗanda ake zargin suna ɗauke da cutar ba su da cutar Ebola.

Duk da haka, ana ci gaba da gwaje-gwaje domin gano ko cututtuka irin su zazzaɓin Lassa ko zazzaɓin Dengue ne suka haddasa alamomin da aka gani.

“Cutar zazzaɓin mai tsanani da ke sa mutum zubar da jini wato ‘Viral Hemorrhagic Fevers’ na daga cikin manyan cututtuka masu haɗari, kuma suna iya bayyana da alamun zazzabi ko amai ko gudawa da kuma zubar jini daga jiki.” in ji KNCDC.

“Waɗannan cututtuka na iya yaɗuwa daga dabbobi zuwa mutane ko kuma daga mutum zuwa mutum ta hanyar jini ko zufa.” hukumar ta ƙra da cewa.

KNCDC ta kuma shawarci jama’ar Kano da “Su kiyaye tsafta ta hanyar wanke hannu akai-akai da sabulu ko abubuwan tsaftace hannu da kauce wa hulɗa da mutanen da ke da zazzabi ko zubar jini ba tare da sanin ko mene ne ba, da kuma gujewa hulɗa da namun daji saboda gujewa kamuwa da cutar.

Haka kuma, ta yi kira da a tabbatar an dafa nama da kyau kafin a ci, sannan a garzaya asibiti idan aka fuskanci alamomin cutar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp