Home Labarai Ƴan bindiga sun sako mutane 40 bayan sulhu da mahukuntan Katsina

Ƴan bindiga sun sako mutane 40 bayan sulhu da mahukuntan Katsina

Taswirar Katsina
Katsina

Aƙalla mutane 40 da aka yi garkuwa da su ne suka shaƙi iskar ƴanci a ƙaramar hukumar Faskari ta jihar Katsina bayan tattaunawa tsakanin ƙasurgumin ɗan bindigar daji Isya Kwashen Garwa da mahukuntan jihar inda yaran ɗan ta’addar suka miƙa mutanen ga hukumomin jihar.

Bayanai sun ce sakin wannan adadi na zuwa ne bayan sakin wasu mutane 30 a Larabar makon jiya da kuma wasu mutum biyu na daban, wanda ke nuna a jumlace ɗan bindigar ya sako mutane 72 daga faro wannan tattaunawa kawo yanzu.

Mahukuntan Katsina na sahun waɗanda ke tattaunawa da ƴan bindiga don kawo ƙarshen tashe-tashen hankulan da jihar ke gani, sai dai a gefe guda ana ci gaba da ganin ta’adin waɗannan ɓatagari.

Mataimakin shugaban karamar hukumar Faskari, Hon. Isiyaku Wada ya tabbatar da sakin mutanen, to sai dai ya buƙaci haɗin-kan jami’an tsaro don tabbatar da samun nasarar wannan sulhu da ke bai wa kowane bangare damar yin walwala.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp