Home Labarai Ƴan bindiga sun sako mutane 40 bayan sulhu da mahukuntan Katsina

Ƴan bindiga sun sako mutane 40 bayan sulhu da mahukuntan Katsina

Taswirar Katsina
Katsina

Aƙalla mutane 40 da aka yi garkuwa da su ne suka shaƙi iskar ƴanci a ƙaramar hukumar Faskari ta jihar Katsina bayan tattaunawa tsakanin ƙasurgumin ɗan bindigar daji Isya Kwashen Garwa da mahukuntan jihar inda yaran ɗan ta’addar suka miƙa mutanen ga hukumomin jihar.

Bayanai sun ce sakin wannan adadi na zuwa ne bayan sakin wasu mutane 30 a Larabar makon jiya da kuma wasu mutum biyu na daban, wanda ke nuna a jumlace ɗan bindigar ya sako mutane 72 daga faro wannan tattaunawa kawo yanzu.

Mahukuntan Katsina na sahun waɗanda ke tattaunawa da ƴan bindiga don kawo ƙarshen tashe-tashen hankulan da jihar ke gani, sai dai a gefe guda ana ci gaba da ganin ta’adin waɗannan ɓatagari.

Mataimakin shugaban karamar hukumar Faskari, Hon. Isiyaku Wada ya tabbatar da sakin mutanen, to sai dai ya buƙaci haɗin-kan jami’an tsaro don tabbatar da samun nasarar wannan sulhu da ke bai wa kowane bangare damar yin walwala.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp