Home Labarai Rundunar ƴan sandan Najeriya ta tabbatar da mutuwar jami’anta a Jihar Benue

Rundunar ƴan sandan Najeriya ta tabbatar da mutuwar jami’anta a Jihar Benue

Rundunar ‘yan sandan Najeriya ta tabbatar da kashe jami’anta uku tare da bacewar wasu bakwai a wani mummunan harin kwantan bauna da aka kai wa rundunar kota-kwananta a jihar Benue.

A ranar Laraba 10 ga watan Satumban 2025 ne, aka kai wani hari makamancinsa a garin Egbe da ke ƙaramar hukumar Yagba ta yamma da ke jihar Kogi, a kusa da kan iyakar ta da jihar Kwara, inda jami’anta uku suka mutu.

Yayin da Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar Kogi, William Aya, ya tabbatar da mutuwar jami’an rundunar guda uku, sannan kwamishinan ‘yan sandan jihar, CP Miller Dantawaye, ya ce an tura tawagar da za ta mayar da martani zuwa yankin.

A wata sanarwa da rundunar ta fitar mai ɗauke da sa hannun jami’in hulɗa da jama’a na rundunar, CSP Benjamin Hundeyin, a ranar Lahadi, ta ce ‘yan sandan sun bayyana cewa lamarin ya faru ne a ranar Juma’a, 19 ga watan Satumbar, 2025, a ƙaramar hukumar Katsina-Ala, inda inda ake kyautata zaton ‘yan bindigar yankin ne suka ƙaddamar da harin.

Kakakin ‘yan sandan ya ce an kama mutane shida da ake zargi a wani samame da ake ci gaba da kai wa kuma suna taimakawa da bayanai masu amfani.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp