Home Labarai Rundunar ƴan sandan Najeriya ta tabbatar da mutuwar jami’anta a Jihar Benue

Rundunar ƴan sandan Najeriya ta tabbatar da mutuwar jami’anta a Jihar Benue

Rundunar ‘yan sandan Najeriya ta tabbatar da kashe jami’anta uku tare da bacewar wasu bakwai a wani mummunan harin kwantan bauna da aka kai wa rundunar kota-kwananta a jihar Benue.

A ranar Laraba 10 ga watan Satumban 2025 ne, aka kai wani hari makamancinsa a garin Egbe da ke ƙaramar hukumar Yagba ta yamma da ke jihar Kogi, a kusa da kan iyakar ta da jihar Kwara, inda jami’anta uku suka mutu.

Yayin da Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar Kogi, William Aya, ya tabbatar da mutuwar jami’an rundunar guda uku, sannan kwamishinan ‘yan sandan jihar, CP Miller Dantawaye, ya ce an tura tawagar da za ta mayar da martani zuwa yankin.

A wata sanarwa da rundunar ta fitar mai ɗauke da sa hannun jami’in hulɗa da jama’a na rundunar, CSP Benjamin Hundeyin, a ranar Lahadi, ta ce ‘yan sandan sun bayyana cewa lamarin ya faru ne a ranar Juma’a, 19 ga watan Satumbar, 2025, a ƙaramar hukumar Katsina-Ala, inda inda ake kyautata zaton ‘yan bindigar yankin ne suka ƙaddamar da harin.

Kakakin ‘yan sandan ya ce an kama mutane shida da ake zargi a wani samame da ake ci gaba da kai wa kuma suna taimakawa da bayanai masu amfani.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp