Home Labarai Nasarar da Daliban Kano suka Samu a NECO kokarin Ganduje ne –...

Nasarar da Daliban Kano suka Samu a NECO kokarin Ganduje ne – Sanusi Kiru

Tsohon Kwamishinan Ilimi na Jihar Kano, Hon. Muhammad Sanusi Kiru, ya taya daliban jihar murna bisa nasarar da suka samu a sakamakon jarabawar kammala makarantun sakandare (NECO) na shekarar 2025.

Wannan na zuwa ne bayan da sakamakon jarabar ya nuna yadda daliban jihar suka zama zakaran gwajin dafia darussan Turanci da Lissafi a fadin Nijeriya.

Ta cikin wata sanarwa da ya sanyawa hannu kuma aka rabata ga manema labarai, Kiru ya ce wannan gagarumar nasara ba wai kawai tasirin sauye-sauyen gwamnatin mai ci ke nuna wa ba, illa alama ce ta irin jarin da tsohon gwamna, Dr. Abdullahi Umar Ganduje, ya zuba a bangaren ilimi daga shekarar 2015 zuwa 2023.

“Ingantattun tsare-tsare da aka aiwatar a wancan lokaci wajen gyara makarantu, horas da malamai da samar da kayan aiki su ne tubalan da daliban suka dogara da su wajen kaiwa ga wannan matsayi,” in ji Kiru.

Ya kara da cewa ba adalci ba ne a jingina nasarar kacokan ga gwamnatin yanzu ba tare da la’akari da irin rawar da aka taka a baya ba, domin irin wadannan sakamako na fito ne daga tsare-tsare masu dogon zango.

Sanusi Kiru ya yaba wa daliban da suka yi fice, tare da jinjinawa malamai, iyaye da duk masu ruwa da tsaki da suka bada gudummawa wajen ganin wannan nasara ta tabbata. Ya kuma bukaci gwamnatin mai ci da ta kara dagewa domin ci gaba da inganta harkar ilimi a Kano, domin amfanin al’umma a nan gaba.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp