Home Labarai Nasarar da Daliban Kano suka Samu a NECO kokarin Ganduje ne –...

Nasarar da Daliban Kano suka Samu a NECO kokarin Ganduje ne – Sanusi Kiru

Tsohon Kwamishinan Ilimi na Jihar Kano, Hon. Muhammad Sanusi Kiru, ya taya daliban jihar murna bisa nasarar da suka samu a sakamakon jarabawar kammala makarantun sakandare (NECO) na shekarar 2025.

Wannan na zuwa ne bayan da sakamakon jarabar ya nuna yadda daliban jihar suka zama zakaran gwajin dafia darussan Turanci da Lissafi a fadin Nijeriya.

Ta cikin wata sanarwa da ya sanyawa hannu kuma aka rabata ga manema labarai, Kiru ya ce wannan gagarumar nasara ba wai kawai tasirin sauye-sauyen gwamnatin mai ci ke nuna wa ba, illa alama ce ta irin jarin da tsohon gwamna, Dr. Abdullahi Umar Ganduje, ya zuba a bangaren ilimi daga shekarar 2015 zuwa 2023.

“Ingantattun tsare-tsare da aka aiwatar a wancan lokaci wajen gyara makarantu, horas da malamai da samar da kayan aiki su ne tubalan da daliban suka dogara da su wajen kaiwa ga wannan matsayi,” in ji Kiru.

Ya kara da cewa ba adalci ba ne a jingina nasarar kacokan ga gwamnatin yanzu ba tare da la’akari da irin rawar da aka taka a baya ba, domin irin wadannan sakamako na fito ne daga tsare-tsare masu dogon zango.

Sanusi Kiru ya yaba wa daliban da suka yi fice, tare da jinjinawa malamai, iyaye da duk masu ruwa da tsaki da suka bada gudummawa wajen ganin wannan nasara ta tabbata. Ya kuma bukaci gwamnatin mai ci da ta kara dagewa domin ci gaba da inganta harkar ilimi a Kano, domin amfanin al’umma a nan gaba.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp