Home Labarai Wata kotun Majistiri a Kano ta bawa Jami’an KAROTA umarni

Wata kotun Majistiri a Kano ta bawa Jami’an KAROTA umarni

Wata kotun tafi da gidanka a jihar Kano ta umarci jami’an hukumar dake lura da zirga-zirgar ababan hawa ta jihar Kano KAROTA da su kasance masu gudanar da ayyukansu cikin gaskiya da rikon Amana.

Mai shari’a Chief Majistire Halima Wali ce tayi umarnin yayin da take yanke hukunci kan wasu daga cikin mutane 82 da aka kama da laifukan karya dokokin hanya a jihar kano.

Wannan na cikin wata sanarwa da kakakin hukumar Abubakar Ibrahim Sharada Anipr ya fitar kuma aka raba manema labarai a jihar Kano.

Wadanda aka yankewa hukuncin sun an same su da laifin karya dokokin hanya da suka hadar da sabawa dokar fitilar bada hannu a manyan titunan kwayar birnin jihar.

Kotunan guda biyu da suka zauna a mahadar Kwanar Sabo da ke kan titin zuwa Maiduguri, da kuma Mahadar Mambayya dake gwammaja a jihar kano karkashin jagorancin Mai shari’a hauwa Abba da Mai Shari’a Halima Wali.

Da yake jawabi ga manema labarai Shugaban hukumar ta KAROTA Hon. Faisal Mahmud Kabir ya yabawa Alkalan kutunan bisa jajircewarsu da sadaukarwa da suke wajin tabbatar da an bi dokokin hukumar.

Haka kuma ya tabbatar da cewa hukumar zata samar da dukkan abinda ake bukata domin gudanar zaman kotunan Tafi da gidan ka yadda ya kamata

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp