Home Labarai Wata kotun Majistiri a Kano ta bawa Jami’an KAROTA umarni

Wata kotun Majistiri a Kano ta bawa Jami’an KAROTA umarni

Wata kotun tafi da gidanka a jihar Kano ta umarci jami’an hukumar dake lura da zirga-zirgar ababan hawa ta jihar Kano KAROTA da su kasance masu gudanar da ayyukansu cikin gaskiya da rikon Amana.

Mai shari’a Chief Majistire Halima Wali ce tayi umarnin yayin da take yanke hukunci kan wasu daga cikin mutane 82 da aka kama da laifukan karya dokokin hanya a jihar kano.

Wannan na cikin wata sanarwa da kakakin hukumar Abubakar Ibrahim Sharada Anipr ya fitar kuma aka raba manema labarai a jihar Kano.

Wadanda aka yankewa hukuncin sun an same su da laifin karya dokokin hanya da suka hadar da sabawa dokar fitilar bada hannu a manyan titunan kwayar birnin jihar.

Kotunan guda biyu da suka zauna a mahadar Kwanar Sabo da ke kan titin zuwa Maiduguri, da kuma Mahadar Mambayya dake gwammaja a jihar kano karkashin jagorancin Mai shari’a hauwa Abba da Mai Shari’a Halima Wali.

Da yake jawabi ga manema labarai Shugaban hukumar ta KAROTA Hon. Faisal Mahmud Kabir ya yabawa Alkalan kutunan bisa jajircewarsu da sadaukarwa da suke wajin tabbatar da an bi dokokin hukumar.

Haka kuma ya tabbatar da cewa hukumar zata samar da dukkan abinda ake bukata domin gudanar zaman kotunan Tafi da gidan ka yadda ya kamata

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp