Home Labarai Wata kotun Majistiri a Kano ta bawa Jami’an KAROTA umarni

Wata kotun Majistiri a Kano ta bawa Jami’an KAROTA umarni

Wata kotun tafi da gidanka a jihar Kano ta umarci jami’an hukumar dake lura da zirga-zirgar ababan hawa ta jihar Kano KAROTA da su kasance masu gudanar da ayyukansu cikin gaskiya da rikon Amana.

Mai shari’a Chief Majistire Halima Wali ce tayi umarnin yayin da take yanke hukunci kan wasu daga cikin mutane 82 da aka kama da laifukan karya dokokin hanya a jihar kano.

Wannan na cikin wata sanarwa da kakakin hukumar Abubakar Ibrahim Sharada Anipr ya fitar kuma aka raba manema labarai a jihar Kano.

Wadanda aka yankewa hukuncin sun an same su da laifin karya dokokin hanya da suka hadar da sabawa dokar fitilar bada hannu a manyan titunan kwayar birnin jihar.

Kotunan guda biyu da suka zauna a mahadar Kwanar Sabo da ke kan titin zuwa Maiduguri, da kuma Mahadar Mambayya dake gwammaja a jihar kano karkashin jagorancin Mai shari’a hauwa Abba da Mai Shari’a Halima Wali.

Da yake jawabi ga manema labarai Shugaban hukumar ta KAROTA Hon. Faisal Mahmud Kabir ya yabawa Alkalan kutunan bisa jajircewarsu da sadaukarwa da suke wajin tabbatar da an bi dokokin hukumar.

Haka kuma ya tabbatar da cewa hukumar zata samar da dukkan abinda ake bukata domin gudanar zaman kotunan Tafi da gidan ka yadda ya kamata

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp