Home Labarai Gwamnatin Kano ta yi gargaɗi kan zazzaɓi mai tsanani da ke sa...

Gwamnatin Kano ta yi gargaɗi kan zazzaɓi mai tsanani da ke sa mutum zubar da jini

Hukumar kula da cututtuka ta jihar Kano KNCDC ta fitar da sanarwar gargadi ga ƴan jihar dangane da rahoton da hukumar kula da cututtuka ta ƙasa (NCDC) ta bayar kan wasu mutane biyu da ake zargin suna ɗauke da cutar zazzaɓi mai tsanani da ke sa mutum zubar da jini a Abuja.

Wannan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da hukumar ta fitar a shafukan sada zumuntarta. Inda ta ce gargaɗi na daga cikin shirin kare lafiyar al’umma, duba da yadda Kano ke da yawan jama’a da kuma hulɗar kasuwanci da tafiye-tafiye zuwa sauran sassan ƙasar.

Sanarwar ta tabbatar da cewa binciken farko ya nuna waɗanda ake zargin suna ɗauke da cutar ba su da cutar Ebola.

Duk da haka, ana ci gaba da gwaje-gwaje domin gano ko cututtuka irin su zazzaɓin Lassa ko zazzaɓin Dengue ne suka haddasa alamomin da aka gani.

“Cutar zazzaɓin mai tsanani da ke sa mutum zubar da jini wato ‘Viral Hemorrhagic Fevers’ na daga cikin manyan cututtuka masu haɗari, kuma suna iya bayyana da alamun zazzabi ko amai ko gudawa da kuma zubar jini daga jiki.” in ji KNCDC.

“Waɗannan cututtuka na iya yaɗuwa daga dabbobi zuwa mutane ko kuma daga mutum zuwa mutum ta hanyar jini ko zufa.” hukumar ta ƙra da cewa.

KNCDC ta kuma shawarci jama’ar Kano da “Su kiyaye tsafta ta hanyar wanke hannu akai-akai da sabulu ko abubuwan tsaftace hannu da kauce wa hulɗa da mutanen da ke da zazzabi ko zubar jini ba tare da sanin ko mene ne ba, da kuma gujewa hulɗa da namun daji saboda gujewa kamuwa da cutar.

Haka kuma, ta yi kira da a tabbatar an dafa nama da kyau kafin a ci, sannan a garzaya asibiti idan aka fuskanci alamomin cutar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp