Home Labarai Gwamnatin Najeriya ta ce za ta ci gaba da ciyo bashi duk...

Gwamnatin Najeriya ta ce za ta ci gaba da ciyo bashi duk da samun ƙarin kuɗaɗen shiga-

Gwamnatin Najeriya ta ce za ta ci gaba da karɓo bashi duk da irin gagarumin tagomashin da ta samu na ƙarin kuɗaɗen shiga a ‘yan watannin nan.

A watan Satumbar da muke ciki kaɗai, Najeriya ta samu kuɗaɗen shiga na Naira tiriliyan 3 da biliyan 640, ƙarin kashi 411 kenan idan aka kwantanta da Naira biliyan 711 da aka samu a watan Mayu.

Adedeji ya ce ciyo bashi fa ba matsala bane, saboda kafin a ciyo sai da majalisar tarayya ta amince da hakan, haka zalika basa zagayewa su karbo wani bayan wanda aka amince ɗin.

Kalaman na Adedeji, na zuwa ne ƙasa da watanni biyu bayan shugaba Bola Tinubu a watan Yuli ta miƙa buƙatar ciyo bashin Dala biliyan 21 da miliyan 500 daga ƙetare.

Kuma ko a makonni 3 da suka gabata, sai da Tinubu ya ce Najeriya ta samu kuɗaɗen shigar da tayi hasashen samu a shekarar 2025, kafin ma lokacin da tayi tsammani, a don haka bazata dogara da ciyo bashi ba a kasafin kuɗi.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp