Home General DSS ta gurfanar da Sowore a kotu kan zargin ‘aibata’ Tinubu a...

DSS ta gurfanar da Sowore a kotu kan zargin ‘aibata’ Tinubu a shafin X

Hukumar tsaro ta DSS a Najeriya ta gurfanar da tsohon ɗan takarar shugaban ƙasar Omoyele Sowore a gaban wata babbar kotun tarayya da ke Abuja a yau, Talata, bisa zargin shi da aibata shugaba Bola Tinubu a shafinsa na X.

Hakazalika, DSS ta gurfanar da manyan kamfanonin sada zumunta na X da Meta a matsayin waɗanda ake ƙara.

Hukumar ta ce waɗannan kamfanoni sun ƙi goge abin da suka kira kalaman ƙarya da cin mutunci da aibata shugaba Tinubu da Sowore ya wallafa a shafinsa na sada zumunta.

Tun a ranar 6 ga watan Satumban 2025 ne DSS ta sanar da cewa ta nemi a rufe ko a dakatar da shafin Sowore a dandalin X bisa zargin cewa yana yaɗa kalamai da za su iya haifar da rikici da barazana ga tsaron ƙasa.

Hukumar ta ce ta ɗauki wannan mataki ne domin kare martabar shugabanci da kuma kare ƙasar daga mummunar tasirin yaɗa labaran ƙarya.

Hukumar ta bayyana cewa kalaman kai tsaye a kan Tinubu barazana ce ga tsaron ƙasar inda ta yi kira ga kamfanin X da ya goge tare da gaggauta rufe ko dakatar da shafin Sowore.

Amma kuma har yanzu X bai rufe shafin nasa ba inda DSS ta zargi kamfanin da rashin bin umarninta dalilin da ya sa ta gurfanar da kamfanin a gaban kotu.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp