Home General DSS ta gurfanar da Sowore a kotu kan zargin ‘aibata’ Tinubu a...

DSS ta gurfanar da Sowore a kotu kan zargin ‘aibata’ Tinubu a shafin X

Hukumar tsaro ta DSS a Najeriya ta gurfanar da tsohon ɗan takarar shugaban ƙasar Omoyele Sowore a gaban wata babbar kotun tarayya da ke Abuja a yau, Talata, bisa zargin shi da aibata shugaba Bola Tinubu a shafinsa na X.

Hakazalika, DSS ta gurfanar da manyan kamfanonin sada zumunta na X da Meta a matsayin waɗanda ake ƙara.

Hukumar ta ce waɗannan kamfanoni sun ƙi goge abin da suka kira kalaman ƙarya da cin mutunci da aibata shugaba Tinubu da Sowore ya wallafa a shafinsa na sada zumunta.

Tun a ranar 6 ga watan Satumban 2025 ne DSS ta sanar da cewa ta nemi a rufe ko a dakatar da shafin Sowore a dandalin X bisa zargin cewa yana yaɗa kalamai da za su iya haifar da rikici da barazana ga tsaron ƙasa.

Hukumar ta ce ta ɗauki wannan mataki ne domin kare martabar shugabanci da kuma kare ƙasar daga mummunar tasirin yaɗa labaran ƙarya.

Hukumar ta bayyana cewa kalaman kai tsaye a kan Tinubu barazana ce ga tsaron ƙasar inda ta yi kira ga kamfanin X da ya goge tare da gaggauta rufe ko dakatar da shafin Sowore.

Amma kuma har yanzu X bai rufe shafin nasa ba inda DSS ta zargi kamfanin da rashin bin umarninta dalilin da ya sa ta gurfanar da kamfanin a gaban kotu.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp