Home General Muna so majalisa ta gaggauta amincewa da sabbin dokokinmu – INEC

Muna so majalisa ta gaggauta amincewa da sabbin dokokinmu – INEC

Shugaban hukumar zaɓe ta kasa INEC, Farfesa Mahmood Yakubu, ya buƙaci majalisar dokokin Najeriya da ta gaggauta amincewa da sabbin sauye-sauyen dokokin zaɓe na ƙasar.

Ya bayyana haka ne a ranar Alhamis a Abuja yayin wata ganawa da tawagar sa ido kan zaɓe ta Tarayyar Turai (EU) ƙarƙashin jagorancin Barry Andrews, wanda shi ma ya jagoranci sa ido a babban zaɓen 2023.

A farkon shekarar nan ne dai hukumar INEC ta aikewa majalisa wasu dokoki da take so a yi gyara da suka haɗa da:

  • Zaɓen wuri (Early Voting)
  • Zaɓen mazauna ƙasashen waje (Diaspora Voting)
  • Gyara amfani da katin zaɓe na dindindin
  • Bai wa INEC damar naɗa shugabannin zaɓe na jihohi
  • Samar da hukumomin sasanta rikicin zaɓe

Farfesa Yakubu ya jaddada cewa amincewa da sabbin dokokin da wuri zai taimaka wa INEC wajen tsara shirye-shirye cikin nasara kafin babban zaɓe na gaba.

Ya bayyana cewa hukumar INEC ta yi nazari sosai kan dukkan shawarwari guda takwas da masu sa ido kan zaɓe ta EU ta bayar da suka shafi hukumar kai tsaye a rahotonsu na zaɓen 2023.

Yakubu ya ce hukumar ta riga ta ɗauki matakai a kan waɗanda ke buƙatar sauye-sauye cikin gida, sannan tana aiki tare da sauran sassa kan shawarwari da suka shafi kowa.

Ya kuma ce hukumar tana jiran kammala nazarin sauye-sauyen doka da majalisar dokoki ke yi.

Shugaban INEC ɗin ya ƙara da cewa shawarwarin EU da na sauran masu sa ido, na cikin muhimman abubuwan da aka yi la’akari da su yayin nazarin bayan zaɓe na 2023.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp