Home Labarai Gwamnatin Najeriya ta ce za ta ci gaba da ciyo bashi duk...

Gwamnatin Najeriya ta ce za ta ci gaba da ciyo bashi duk da samun ƙarin kuɗaɗen shiga-

Gwamnatin Najeriya ta ce za ta ci gaba da karɓo bashi duk da irin gagarumin tagomashin da ta samu na ƙarin kuɗaɗen shiga a ‘yan watannin nan.

A watan Satumbar da muke ciki kaɗai, Najeriya ta samu kuɗaɗen shiga na Naira tiriliyan 3 da biliyan 640, ƙarin kashi 411 kenan idan aka kwantanta da Naira biliyan 711 da aka samu a watan Mayu.

Adedeji ya ce ciyo bashi fa ba matsala bane, saboda kafin a ciyo sai da majalisar tarayya ta amince da hakan, haka zalika basa zagayewa su karbo wani bayan wanda aka amince ɗin.

Kalaman na Adedeji, na zuwa ne ƙasa da watanni biyu bayan shugaba Bola Tinubu a watan Yuli ta miƙa buƙatar ciyo bashin Dala biliyan 21 da miliyan 500 daga ƙetare.

Kuma ko a makonni 3 da suka gabata, sai da Tinubu ya ce Najeriya ta samu kuɗaɗen shigar da tayi hasashen samu a shekarar 2025, kafin ma lokacin da tayi tsammani, a don haka bazata dogara da ciyo bashi ba a kasafin kuɗi.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp