Home Labarai Gwamnatin Najeriya ta ce za ta ci gaba da ciyo bashi duk...

Gwamnatin Najeriya ta ce za ta ci gaba da ciyo bashi duk da samun ƙarin kuɗaɗen shiga-

Gwamnatin Najeriya ta ce za ta ci gaba da karɓo bashi duk da irin gagarumin tagomashin da ta samu na ƙarin kuɗaɗen shiga a ‘yan watannin nan.

A watan Satumbar da muke ciki kaɗai, Najeriya ta samu kuɗaɗen shiga na Naira tiriliyan 3 da biliyan 640, ƙarin kashi 411 kenan idan aka kwantanta da Naira biliyan 711 da aka samu a watan Mayu.

Adedeji ya ce ciyo bashi fa ba matsala bane, saboda kafin a ciyo sai da majalisar tarayya ta amince da hakan, haka zalika basa zagayewa su karbo wani bayan wanda aka amince ɗin.

Kalaman na Adedeji, na zuwa ne ƙasa da watanni biyu bayan shugaba Bola Tinubu a watan Yuli ta miƙa buƙatar ciyo bashin Dala biliyan 21 da miliyan 500 daga ƙetare.

Kuma ko a makonni 3 da suka gabata, sai da Tinubu ya ce Najeriya ta samu kuɗaɗen shigar da tayi hasashen samu a shekarar 2025, kafin ma lokacin da tayi tsammani, a don haka bazata dogara da ciyo bashi ba a kasafin kuɗi.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp