Home Labarai Gwamnatin Najeriya ta ce za ta ci gaba da ciyo bashi duk...

Gwamnatin Najeriya ta ce za ta ci gaba da ciyo bashi duk da samun ƙarin kuɗaɗen shiga-

Gwamnatin Najeriya ta ce za ta ci gaba da karɓo bashi duk da irin gagarumin tagomashin da ta samu na ƙarin kuɗaɗen shiga a ‘yan watannin nan.

A watan Satumbar da muke ciki kaɗai, Najeriya ta samu kuɗaɗen shiga na Naira tiriliyan 3 da biliyan 640, ƙarin kashi 411 kenan idan aka kwantanta da Naira biliyan 711 da aka samu a watan Mayu.

Adedeji ya ce ciyo bashi fa ba matsala bane, saboda kafin a ciyo sai da majalisar tarayya ta amince da hakan, haka zalika basa zagayewa su karbo wani bayan wanda aka amince ɗin.

Kalaman na Adedeji, na zuwa ne ƙasa da watanni biyu bayan shugaba Bola Tinubu a watan Yuli ta miƙa buƙatar ciyo bashin Dala biliyan 21 da miliyan 500 daga ƙetare.

Kuma ko a makonni 3 da suka gabata, sai da Tinubu ya ce Najeriya ta samu kuɗaɗen shigar da tayi hasashen samu a shekarar 2025, kafin ma lokacin da tayi tsammani, a don haka bazata dogara da ciyo bashi ba a kasafin kuɗi.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp