Home Labarai Majalisar dokokin Nijeriya na shirin sauya lokaci zaben shugaban kasa

Majalisar dokokin Nijeriya na shirin sauya lokaci zaben shugaban kasa

Majalisar Dokokin Najeriya ta bayar da shawarar sauya lokacin gudanar da zaɓen shugaban ƙasar zuwa watan Nuwamban 2026 maimakon Fabrairun 2027.

Shawarar na ƙunshe cikin daftarin ƙudurin dokar zaɓe ta 2025, da aka gabatar ranar Litinin a lokacin zaman sauraron jin ra’ayin jama’a na haɗin gwiwa tsakanin kwamitocin zaɓe na majalisun dokokin biyu da aka yi a Abuja.

Ƙudurin, ya nemi a sauya dokar zaɓe ta 2022 tare da amincewa da sabuwar dokar zaɓe ta 2025.

A cewar daftarin, ”za a gudanar da zaɓukan shugaban ƙasa da na gwamnoni ƙasa da kwana 185 kafin ƙarewar wa’adin waɗanda ke riƙe da muƙaman”.

Ƴanmajalisar sun ce manufar sauyin shi ne tabbatar da kammala duka shari’o’in ƙorafe-ƙorafen zaɓe kafin ranar 29 ga watan Mayun 2027 da za a rantsar da shugaban ƙasa da gwamnoni.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp