Home Labarai Gwamnan Enugu ya koma APC bayan ficewa daga PDP

Gwamnan Enugu ya koma APC bayan ficewa daga PDP

Gwamnan jihar Enugu, Peter Mbah ya fice daga jam’iyyarsa ta PDP tare da komawa APC mai mulkin Najeriya.

Mista Mbah ya bayyana haka ne a wani taron manema labarai da ya shirya a fadar gwamnanatin jihar da ke birnin Enugu.

“Bayan dogon lokaci da muka ɗauka muna nazari, a yau mun yanke shawarar ficewa daga PDP tare da komawa APC,” kamar yadda gwamnan ya bayyana.

Mbah ya ce ya koma APC ne saboda kyawawan manufofin jam’iyyar da ayyukan ci gaba da take samarwa a Najeriya da ma jiharsa ta Enugu.

Gwamnan ya ce yana da ƙwarin gwiwar cewa komawarsa APC za ta samar wa jihar ƙarin damarmaki da ci gaba.

Taron ya samu halartar manyan ƴansiyasar jihar da suka haɗa da mataimakin gwamnan jihar, Barr Ifeanyi Ossai da tsoffin gwamnonin jihar, Sullivan Chime da Rt Hon. ifeanyi Ugwuanyi,da Tsohon Shugaban Majalisar Dattawan Najeriya, Chief Ken Nnamani, da tsoffin ƴanmajalisar tarayya daga jihar da kuma masu ci, da shugaban majalisar dokokin jihar da shugaban jam’iyyar APC na jihar, da sauran muƙarraban gwamnatinsa, kamar yadda mataimaki na musamman ga gwamnan kan kafofin yaɗa labarai, Dan Nwomeh ya wallafa a shafinsa na X.

Dama dai tun jiya wasu daga cikin kwamishinonin gwamnan suka fice daga PDP tare da komawa APC.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp