Home Labarai Majalisar dokokin Nijeriya na shirin sauya lokaci zaben shugaban kasa

Majalisar dokokin Nijeriya na shirin sauya lokaci zaben shugaban kasa

Majalisar Dokokin Najeriya ta bayar da shawarar sauya lokacin gudanar da zaɓen shugaban ƙasar zuwa watan Nuwamban 2026 maimakon Fabrairun 2027.

Shawarar na ƙunshe cikin daftarin ƙudurin dokar zaɓe ta 2025, da aka gabatar ranar Litinin a lokacin zaman sauraron jin ra’ayin jama’a na haɗin gwiwa tsakanin kwamitocin zaɓe na majalisun dokokin biyu da aka yi a Abuja.

Ƙudurin, ya nemi a sauya dokar zaɓe ta 2022 tare da amincewa da sabuwar dokar zaɓe ta 2025.

A cewar daftarin, ”za a gudanar da zaɓukan shugaban ƙasa da na gwamnoni ƙasa da kwana 185 kafin ƙarewar wa’adin waɗanda ke riƙe da muƙaman”.

Ƴanmajalisar sun ce manufar sauyin shi ne tabbatar da kammala duka shari’o’in ƙorafe-ƙorafen zaɓe kafin ranar 29 ga watan Mayun 2027 da za a rantsar da shugaban ƙasa da gwamnoni.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp