Home Labarai Majalisar dokokin Nijeriya na shirin sauya lokacin zaben shugaban Kasa

Majalisar dokokin Nijeriya na shirin sauya lokacin zaben shugaban Kasa

Majalisar Dokokin Najeriya ta bayar da shawarar sauya lokacin gudanar da zaɓen shugaban ƙasar zuwa watan Nuwamban 2026 maimakon Fabrairun 2027.

Shawarar na ƙunshe cikin daftarin ƙudurin dokar zaɓe ta 2025, da aka gabatar ranar Litinin a lokacin zaman sauraron jin ra’ayin jama’a na haɗin gwiwa tsakanin kwamitocin zaɓe na majalisun dokokin biyu da aka yi a Abuja.

Ƙudurin, ya nemi a sauya dokar zaɓe ta 2022 tare da amincewa da sabuwar dokar zaɓe ta 2025.

A cewar daftarin, ”za a gudanar da zaɓukan shugaban ƙasa da na gwamnoni ƙasa da kwana 185 kafin ƙarewar wa’adin waɗanda ke riƙe da muƙaman”.

Ƴanmajalisar sun ce manufar sauyin shi ne tabbatar da kammala duka shari’o’in ƙorafe-ƙorafen zaɓe kafin ranar 29 ga watan Mayun 2027 da za a rantsar da shugaban ƙasa da gwamnoni.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp