Home General Gwamnatin Najeriya ta cire darasin Lissafi cikin sharuɗan samun gurbin karatun Jami’a...

Gwamnatin Najeriya ta cire darasin Lissafi cikin sharuɗan samun gurbin karatun Jami’a ga wasu ɗaliban

Gwamnatin Najeriya ta cire wajibcin cin darasin lissafi cikin sharuɗaɗan samun gurbin karatu a jami’a ga ɗaliban da za su karanci kwasa-kwasan da na na kimiyya ba.

Cikin wata sanarwar da ma’aikatar ilimin ƙasar ta fitar ta ce daga yanzu ɗaliban da ke son karanta kwasa-kwasan da ba su da kusanci da kimiyya ko fasaha ba, cin darasin lissafi a sakandire bai zame musu wajibi ba.

Kwasa-kwasan sun haɗa da nazarin ilimin harsuna da zane-zane da nazarin wasannin kwaikwayo da kaɗe-kaɗe, amma dole sai sun ci darasin Ingilishi a sakandire.

Sai dai sanarwar ta jaddada wajibcin darasin lissafin ga sauran kwasa-kwasan da suka shafi kimiyya da fasaha da nazarin zamantakewa.

Ma’aikatar ta ce ta ɗauki matakin ne domin ɗalibai da dama su riƙa samun damar shiga jami’a.

”Matakin zai samar da ƙarin guraben karatu 300,000 a kowace shekara, domin rage yawan ɗaliban da ba sa samun guraben karatu, tare da ƙarfafa sana’o’in dogaro da kai”, in ji sanarwar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp