Home General Gwamnatin Najeriya ta cire darasin Lissafi cikin sharuɗan samun gurbin karatun Jami’a...

Gwamnatin Najeriya ta cire darasin Lissafi cikin sharuɗan samun gurbin karatun Jami’a ga wasu ɗaliban

Gwamnatin Najeriya ta cire wajibcin cin darasin lissafi cikin sharuɗaɗan samun gurbin karatu a jami’a ga ɗaliban da za su karanci kwasa-kwasan da na na kimiyya ba.

Cikin wata sanarwar da ma’aikatar ilimin ƙasar ta fitar ta ce daga yanzu ɗaliban da ke son karanta kwasa-kwasan da ba su da kusanci da kimiyya ko fasaha ba, cin darasin lissafi a sakandire bai zame musu wajibi ba.

Kwasa-kwasan sun haɗa da nazarin ilimin harsuna da zane-zane da nazarin wasannin kwaikwayo da kaɗe-kaɗe, amma dole sai sun ci darasin Ingilishi a sakandire.

Sai dai sanarwar ta jaddada wajibcin darasin lissafin ga sauran kwasa-kwasan da suka shafi kimiyya da fasaha da nazarin zamantakewa.

Ma’aikatar ta ce ta ɗauki matakin ne domin ɗalibai da dama su riƙa samun damar shiga jami’a.

”Matakin zai samar da ƙarin guraben karatu 300,000 a kowace shekara, domin rage yawan ɗaliban da ba sa samun guraben karatu, tare da ƙarfafa sana’o’in dogaro da kai”, in ji sanarwar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
https://nnn.ng/image-compressor/
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp