Tinubu ya buƙaci majalisar dattawa ta amince da naɗin Joash Amupitan

Shugaban Najeriya, Bola Tinubu ya aike wa majalisar dattawan ƙasar wasiƙar neman tantance tare da tabbatar da naɗin Farfesa Joash Amupitan (SAN) a matsayin sabon shugaban hukumar zaɓen ƙasar, INEC.

Shugaban Majalisar Dattawan ƙasar, Sanata Godswill Akapbio ne ya bayyana haka, yayin da ya karanto wasiƙar Shugaba Tinubu a zaman majalisar na ranar Talata.

Matakin na zuwa ne bayan amincewar majalisar magabatan ƙasar a makon da ya gabata.

Shugaba Tinubu ya buƙaci ƴanmajalisar su bai wa tantancewar ”muhimmancin gaske”.

Tinubu ya naɗa Farfesa Amupitan ne bayan ƙarewar wa’adin tsohon shugaban hukumar, Farfesa Mahmud Yakubu.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com