Home Labarai Gwamnan jihar Bayelsa, ya fice daga jam’iyyarsa ta PDP.

Gwamnan jihar Bayelsa, ya fice daga jam’iyyarsa ta PDP.

Gwamnan jihar Bayelsa, Douye Diri ya fice daga jam’iyyarsa ta PDP; Diri ya bayyana haka ne ranar Laraba a gidan gwamnatin jihar da ke birnin Yenagoa lokacin taron majalisar zartarwarsa.

Cikin wata sanarwar ta sakataren yada labaran gwamnan, Daniel Alabrah ya wallafa a shafinsa na Facebook ya ce gwamnan ya fice daga PDP ne tare da ƴan majalisar dokokin jihar 19, ciki har da kakakin majalisar.

Kawo yanzu dai Gwamnan bai bayyana jam’iyyar da ya koma ba.

Ficewar gwamnan na zuwa ne kwana guda bayan da takwaransa na Enugu, Peter Mbah, ya fice daga PDPn tare da komawa APC.

A wannan shekarar kaɗai babban jam’iyyar hamayyyar ta PDP ta rasa gwamnoni uku, wani abu da masana ke kallo a matsayin babbar barazana ga jam’iyyar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp