Home Labarai Dalilin da ya sa Amnesty ke neman a soke hukuncin kisa a...

Dalilin da ya sa Amnesty ke neman a soke hukuncin kisa a Najeriya

Ƙungiyar kare haƙƙin bil’adama ta Amnesty International ta yi kira ga hukumomin Nijeriya da su soke hukuncin kisa a ƙasar.

Manajar shirye-shirye ta ƙungiyar, Mrs Barbara Magaji ce ta bayyana hakan a Abuja lokacin da take jawabi a taron masu ruwa da tsaki a Ranar Yaƙi da Hukuncin Kisa ta Duniya.

Ƙungiyar ce dai ta shira taron da haɗin gwiwar ofishin jakadancin Faransa a ƙasar.

Barbara Magaji ta buƙaci a cire dokokin da suka tanadi hukunce-hukuncen kisa daga kundin tsarin mulkin ƙasar da kuma dokokin wasu jihohin ƙasar.

Ta ce ya kamata majalisar dokokin ƙasar ta duba yiwuwar soke hukuncin kisa ga duka manyan laifukan da aka tanadar wa hukuncin a kundin tsarin mulkin ƙasar.

“Babu wata hujja da ke nuna cewa hukuncin kisa na rage aukuwar manyan laifukan”, in ji ta.

A yanzu haka dai jihohin ƙasar 26 da Abuja ne suke da dokokin da suka tanadin hukuncin kisa ga laifukan da suka shafi garkuwa da mutane da fashi da satar shanu da tsafi.

“Duk da tanadin hukuncin kisa a waɗannan jihohin, amma kullum ana ci gaba da samun ƙaruwar irin waɗannan laifukan, musamman garkuwa a mutane da fashi da ma sauran laifukan.”

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
https://nnn.ng/image-compressor/
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp