Home General Majalisar Dattawan Najeriya ta tabbatar da Amupitan a matsayin shugaban INEC

Majalisar Dattawan Najeriya ta tabbatar da Amupitan a matsayin shugaban INEC

Majalisar Dattawan Najeriya ta tabbatar da Farfesa Joash Amupitan, a matsayin shugaban hukumar zaɓe ta ƙasar INEC.

Majalisar ƙarƙashin jagorancin shugabanta Godswill Akpabio ta tabbatar da Amupitan ne bayan kammala tantance shi, inda ya amsa tambayoyin da ƴan majalisar suka yi masa.

Nan gaba kaɗan ne ake sa ran shugaba Bola Tinubu zai rantsar da shi domin kama aiki gadan-gadan.

A ranar 7 ga watan da muke ciki na Oktoba ne tsohon shugaban hukumar, Farfesa Mahmoud Yakubu ya kammala wa’adin mulkinsa na biyu a matsayin shugaban hukumar ta INEC, bayan shafe shekaru 10.

Tun a watan Oktoban 2015 ne marigayi tsohon shugaban Najeriya, Muhamamdu Buhari ya naɗa Farfesa Mahmoud Yakubu, a matsayin shugaban hukumar INEC, kana ya sabunta naɗin nasa a shekarar 2020.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp