Home Labarai Dalilin da ya sa Amnesty ke neman a soke hukuncin kisa a...

Dalilin da ya sa Amnesty ke neman a soke hukuncin kisa a Najeriya

Ƙungiyar kare haƙƙin bil’adama ta Amnesty International ta yi kira ga hukumomin Nijeriya da su soke hukuncin kisa a ƙasar.

Manajar shirye-shirye ta ƙungiyar, Mrs Barbara Magaji ce ta bayyana hakan a Abuja lokacin da take jawabi a taron masu ruwa da tsaki a Ranar Yaƙi da Hukuncin Kisa ta Duniya.

Ƙungiyar ce dai ta shira taron da haɗin gwiwar ofishin jakadancin Faransa a ƙasar.

Barbara Magaji ta buƙaci a cire dokokin da suka tanadi hukunce-hukuncen kisa daga kundin tsarin mulkin ƙasar da kuma dokokin wasu jihohin ƙasar.

Ta ce ya kamata majalisar dokokin ƙasar ta duba yiwuwar soke hukuncin kisa ga duka manyan laifukan da aka tanadar wa hukuncin a kundin tsarin mulkin ƙasar.

“Babu wata hujja da ke nuna cewa hukuncin kisa na rage aukuwar manyan laifukan”, in ji ta.

A yanzu haka dai jihohin ƙasar 26 da Abuja ne suke da dokokin da suka tanadin hukuncin kisa ga laifukan da suka shafi garkuwa da mutane da fashi da satar shanu da tsafi.

“Duk da tanadin hukuncin kisa a waɗannan jihohin, amma kullum ana ci gaba da samun ƙaruwar irin waɗannan laifukan, musamman garkuwa a mutane da fashi da ma sauran laifukan.”

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp