Home Labarai Tinubu ya taya Kwankwaso munar cika shekaru 69 a duniya

Tinubu ya taya Kwankwaso munar cika shekaru 69 a duniya

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya aika sakon taya murna ga tsohon gwamnan Jihar Kano kuma jagoran jam’iyyar NNPP, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, yayin da yake bikin cikar shekarar 69 da haihuwar a ranar 21 ga Oktoba, 2025.

A wata sanarwa da mai ba shugaban ƙasa shawara kan harkokin yada labarai Bayo Onanuga, ya fitar a ranar Litinin, Shugaba Tinubu ya yaba da gudunmawar da Sanata Kwankwaso ya bayar wajen ci gaban ƙasa ta fannoni daban-daban, ciki har da kasancewarsa Mataimakin Kakakin Majalisar Wakilai a zamanin jamhuriya ta uku da Ministan Tsaro da Gwamnan Jihar Kano sau biyu, da kuma Sanata mai wakiltar Kano ta Tsakiya.

Shugaban ƙasa ya bayyana cewa, tasirin siyasar Kwankwaso a Arewacin ƙasar, musamman a Kano, na nuni da irin siyasar jin ƙai da kishin jama’a da ya gada daga marigayi Malam Aminu Kano da marigayi Alhaji Abubakar Rimi.

“Sanata Kwankwaso aboki ne kuma abokin aiki wanda muka yi aiki tare a majalisar dokoki ta tarayya a shekarar 1992, sannan muka zama gwamnoni a shekarar 1999. Mun kuma yi aiki tare wajen kafa jam’iyyar APC. Ko da yake daga baya ya bar jam’iyyar don kafa NNPP, abin lura ne cewa har yanzu yana cikin tafiyar ci gaba,” in ji Shugaba Tinubu.

A daidai lokacin da ake ta jita-jita game da yiwuwar sabuwar dangantaka ko sauya sheka tsakanin manyan ‘yan siyasa, masu lura da al’amura sun bayyana sakon na Tinubu a matsayin alamar gina gada da kuma ƙarfafa zumunta a siyasa.

Shugaban ƙasa ya yi wa Sanata Kwankwaso fatan alheri, lafiya, da ƙarin shekaru masu amfani ga ƙasa da al’umma.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp