Home Labarai Jami’ar ABU ta musanta labarin samar da makamin Nukiliya

Jami’ar ABU ta musanta labarin samar da makamin Nukiliya

Jami’ar Ahmadu Bello da ke Zariya (ABU) ta musanta wani faifan bidiyo da ke yawo a kafafen sada zumunta da ke zarginta da hannu a cikin aikin ƙirƙirar makaman nukiliya a Najeriya.

Daraktan yada labarai na jami’ar, Auwalu Umar, ya bayyana a wata sanarwa da aka fitar a ranar Asabar cewa bidiyon da aka ƙirƙira ta hanyar AI ba gaskiya ba ne, kuma manufarsa ita ce yaudarar jama’a game da shirin makamashin nukiliya a Najeriya.

Ya ce zargin cewa masana na ABU sun taɓa samun kayan aikin ƙirƙirar makami daga cibiyar AQ Khan ta Pakistan ko yin gwajin uranium a Kaduna a shekarun 1980 ba gaskiya bane .

Umar ya ƙara da cewa a lokacin da ake zargin, yawancin masana a cibiyar binciken makamashin nukiliya ta jami’ar (CERT) suna ci gaba da karatu a ƙasashen waje, kuma babu wata shaida da ke nuna an taɓa yin aikin da ya saba wa doka.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp