Gwamnatin Filato ta rufe makarantun jihar saboda tsaro

Rahotannin daga jihar Filato na bayyana cewa Ma’aikatar ilimi ta jihar ta bayar da umarnin rufe duka makarantun jihar na furamare da sakandire sakamakon ƙaruwar matsalar satar ɗalibai a ƙasar.

Hukumar Ilimi a matakin farko ta jihar, PSUBEB ta bayyana ɗaukar matakin a matsayin matakin kariya ga ɗaliban jihar.

Matakin na zuwa ne bayan sace ɗaliban sakandiren Papiri a jihar Neja, kwana biyar bayan sace ɗalibai 25 na makarantar ƴanmata a jihar Kebbi.

Ma’aikatar ilimin jihar ta ce matakin na wucin-gadi ne kuma ya zama dole, la’akari da halin da ake ciki.

Cikin sanarwar da ma’aikatar ta fitar ta buƙaci duka masu ruwa da tsaki a harkar makarantu su yi biyayya wa umarnin.

Matakin ya shafi duka makarantun sakandire na ƙananan sakandire da na furamare.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com