Home Labarai Dalibai 24 da ‘yan bindiga suka sace a Kebbi sun shaƙi iskar...

Dalibai 24 da ‘yan bindiga suka sace a Kebbi sun shaƙi iskar ‘yanci

Gwamnatin Najeriya ta sanar da cewa, jami’an tsaro sun samu nasarar ceto ɗalibai mata 24 da ‘yan bindiga suka sace a makarantar sakandiren Maga dake jihar Kebbi a makon da ya gabata.

A ranar 17 ga watan Nuwamba da sanyin safiya ne ‘yan bindigar su ka kai hari makarantar tare da yin garkuwa da ‘yan matan, ‘yan sa’o’i bayan barin dakarun ƙasar daga yankin.

Harin na Kebbi ya ta’azzara matsalar tsaro a Najeriya, inda wasu mahara na daban suka afkawa yankin Eruku na Kwara tare da sace masu ibada kodayake an samu nasarar ceto dukkaninsu.

Haka zalika, Ƙungiyar Kiristocin Najeriya ta ce 50 daga cikin ɗalibai fiye da 300 da ‘yan bindiga suka sace a makarantar Katolika dake Neja sun shaƙi iskar ‘yanci.

Shugaba Tinubu ya yabawa jami’an tsaron ƙasar da ƙoƙarin da su ke yi, tare da kira na su jajirce don ceto suaran ɗaliban da har yanzu ke hannun ‘yan bindiga.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp