Gwamnonin arewa sun nanata buƙatar kafa ƴansandan jihohi

Ƙungiyar gwamnonin arewacin Najeriya ta sake nanata buƙatar kafa ƴansandan jihohi domin magance matsalolin da yankin ke fuskanta.

Cikin sanarwar bayan taro da ƙungiyar ta fitar bayan kammala taron da ta gudanar a Kaduna, gwamnonin sun yi kira ga majalisar dokokin Najeriya da na jihohi su ɗauki matakan tabbatar da hakan.

Matakin gwamnonin na zuwa ne kwanaki bayan da Shugaban ƙasar Bola Tinubu ya bayar da umarnin ɗaukar sabbin ƴansanda domin magance matsalolin tsaron da ƙasar ke fuskanta.

Cikin wata sanarwa da Shugaba Tinubu ya fitar a makon da ya gabata ya ce zai duba yiwuwar amincewa da kafa ƴansandan jihohin.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com