Home Labarai Gwamnatin Kano ta jaddada aiwatar da dokar hana sana’ar achaɓa a jihar

Gwamnatin Kano ta jaddada aiwatar da dokar hana sana’ar achaɓa a jihar

Gwamnatin jihar Kano ta sanar da jaddada aiwatar da dokar hana sana’ar achaɓa ta shekarar 2013, wani mataki da ta ce zai taimaka wajen kare tsaro da rage laifuka, da tabbatar da doka da oda a fadin jihar.

Ma’aikatar Shari’a ta bayyana cewa dokar, wadda ta dade tana nan daram kuma za a ci gaba da aiwatar da ita sosai.

Wannan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwar da babban mai bai wa gwamnan jihar Shawara Kan Harkokin Labarai na Ma’aikatar Shari’a ya fitar

Babban lauyan jiharkuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru Maude, SAN, ya buƙaci jama’a musamman masu baburan haya wata acaɓa da su yi biyayya ga tanade-tanaden dokar.

Ya tunatar da cewa “Dokar ba sabuwa ba ce, kuma dole a kiyaye ta domin amfanin kowa da kowa.”

A cewarsa, gwamnatin jihar ba za ta lamunci karya dokar ba, musamman a yankunan da aka haramta acaɓa.

Dokar ta hana achaɓa a cikin wasu muhimman ƙananan hukumomin birnin da suka haɗa da Kano Municipal, Gwale, Dala, Nassarawa, Tarauni, Ungogo (Jido), Dawakin Kudu (Tamburawa, Gurjiya da Jido Ward), Fagge da Kumbotso.

Haka kuma, dokar ta tanadi hukunci mai tsauri ga masu karya ta, wanda ya haɗa da ɗaurin watanni shida, tara na Naira 10,000 da kuma yiwuwar ƙwace babur gaba ɗaya.

Ga direbobin da ke aiki a yankunan da aka amince da yin achaɓa, gwamnatin ta nanata wajabcin yin rajista da mai unguwa da sashen ayyuka na ƙaramar hukuma da kuma DPO na yankin su.

Gwamnatin jihar ta yi kira ga direbobi da fasinjoji da shugabannin al’umma da ƙungiyoyin sufuri da su tabbatar da cikakken bin dokar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp