Home Labarai Gwamnatin Kano ta jaddada aiwatar da dokar hana sana’ar achaɓa a jihar

Gwamnatin Kano ta jaddada aiwatar da dokar hana sana’ar achaɓa a jihar

Gwamnatin jihar Kano ta sanar da jaddada aiwatar da dokar hana sana’ar achaɓa ta shekarar 2013, wani mataki da ta ce zai taimaka wajen kare tsaro da rage laifuka, da tabbatar da doka da oda a fadin jihar.

Ma’aikatar Shari’a ta bayyana cewa dokar, wadda ta dade tana nan daram kuma za a ci gaba da aiwatar da ita sosai.

Wannan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwar da babban mai bai wa gwamnan jihar Shawara Kan Harkokin Labarai na Ma’aikatar Shari’a ya fitar

Babban lauyan jiharkuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru Maude, SAN, ya buƙaci jama’a musamman masu baburan haya wata acaɓa da su yi biyayya ga tanade-tanaden dokar.

Ya tunatar da cewa “Dokar ba sabuwa ba ce, kuma dole a kiyaye ta domin amfanin kowa da kowa.”

A cewarsa, gwamnatin jihar ba za ta lamunci karya dokar ba, musamman a yankunan da aka haramta acaɓa.

Dokar ta hana achaɓa a cikin wasu muhimman ƙananan hukumomin birnin da suka haɗa da Kano Municipal, Gwale, Dala, Nassarawa, Tarauni, Ungogo (Jido), Dawakin Kudu (Tamburawa, Gurjiya da Jido Ward), Fagge da Kumbotso.

Haka kuma, dokar ta tanadi hukunci mai tsauri ga masu karya ta, wanda ya haɗa da ɗaurin watanni shida, tara na Naira 10,000 da kuma yiwuwar ƙwace babur gaba ɗaya.

Ga direbobin da ke aiki a yankunan da aka amince da yin achaɓa, gwamnatin ta nanata wajabcin yin rajista da mai unguwa da sashen ayyuka na ƙaramar hukuma da kuma DPO na yankin su.

Gwamnatin jihar ta yi kira ga direbobi da fasinjoji da shugabannin al’umma da ƙungiyoyin sufuri da su tabbatar da cikakken bin dokar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp