Home Labarai Ministan Tsaro Badaru Abubakar ya yi murabus

Ministan Tsaro Badaru Abubakar ya yi murabus

Ministan Tsaron Najeriya, Alhaji Mohammed Badaru Abubakar, ya yi murabus daga mukaminsa nan take, yana mai bayyana dalilan lafiya a matsayin abin da ya tilasta masa yin hakan.

Wannan na kunshe ne ta cikin wata sanarwa da maitamaka shugaban kasa kan harkokin yada labarai da dabaru Bayo Onanuga ya fitar wadda ta ce a cikin  wata wasika mai dauke da kwana watan 1 ga Disamba, wadda aka aika wa Shugaba Bola Tinubu, tsohon ministan ya ce dole ne ya bar kujerar don kula da lafiyarsa. Shugaba Tinubu ya karɓi murabus ɗin nasa tare da yaba masa kan hidimar da ya yi wa ƙasa.

Ana sa ran Shugaban Ƙasa zai sanar da Majalisar Dattawa sunan wanda zai maye gurbin Badaru cikin mako mai zuwa.

Badaru Abubakar, mai shekaru 63, ya yi gwamna a Jihar Jigawa na zango biyu daga 2015 zuwa 2023, kafin a naɗa shi Ministan Tsaro a ranar 21 ga Agusta, 2023.

Murabus ɗinsa ya zo ne a daidai lokacin da Shugaba Tinubu ya ayyana dokar ta-baci kan harkokin tsaro a fadin ƙasa, inda ake jiran ƙarin bayani kan matakan da gwamnati za ta dauka nan gaba.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp