Home Labarai Gwamnan Kano ya magantu ka matsalar tsaro a jihar

Gwamnan Kano ya magantu ka matsalar tsaro a jihar

Gwamnatin Jihar Kano ta sake tabbatarwa mazauna jihar cewa al’amuran tsaro suna tafiya yadda ya kamata, kuma babu wata barazana da ya kamata ta tayar da hankalin jama’a.

Wannan na kunshe ne cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sunusi Bature Dawakin Tofa, ya PRNigeria a safiyar litinin.

Sanarwar ta kara da cewa gwamnan ya bayar da tabbacin ne bayan taron majalisar tsaron jihar da aka yi a ranar Lahadi tare da manyan jami’an tsaro, inda aka sake jaddada kudurin gwamnati na tabbatar da zaman lafiya a dukkan yankunan jihar.

Gwamnatin ta ce duk wani rahoto da ke yawo a kafafen sada zumunta na cewa akwai gagarumar barazanar tsaro a Kano, ba shi da tushe balle makama. Ta ce babu wani sahihin bayanan asiri da ke nuna akwai matsalar tsaro da ta taso ko ta gabatowa a jihar .

Sanarwar ta jaddada cewa gwamnati ba za ta lamunci yada bayanan ƙarya da nufin tayar da hankalin jama’a ba, tare da gargadin cewa irin wannan ɗabi’a na iya janyo hukunci daga hukumomi.

Gwamnatin ta bayyana cewa tana aiki kafaɗa da kafaɗa da hukumomin tsaro, tare da tabbatar da cewa jami’an tsaro sun kasance cikin shiri, kuma an tura su muhimman wurare, suna aiki ba dare ba rana domin tabbatar da zaman lafiya a Kano .

Sanarwar ta kara da cewa an sanya dukkan sassan Kano cikin tsauraran matakan sa ido, tare da ingantaccen tsarin tsaro da ke aiki yadda ya kamata.

Gwamnatin ta roki jama’a su kwantar da hankalinsu, su guji yada jita-jita a kafafen sada zumunta. Ta kuma yi gargaɗin cewa masu yada labaran ƙarya su daina, domin hakan na iya jawo wa mai yi hukunci.

Gwamna Abba Kabir Yusuf ya tabbatar da cewa gwamnati na kara inganta ayyukan leken asiri, haɗin kai tsakanin hukumomin tsaro, da kuma sabunta dabarun tsaro na zamani a fadin jihar Kano

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp