Home Labarai Gwamnan Kano ya magantu ka matsalar tsaro a jihar

Gwamnan Kano ya magantu ka matsalar tsaro a jihar

Gwamnatin Jihar Kano ta sake tabbatarwa mazauna jihar cewa al’amuran tsaro suna tafiya yadda ya kamata, kuma babu wata barazana da ya kamata ta tayar da hankalin jama’a.

Wannan na kunshe ne cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sunusi Bature Dawakin Tofa, ya PRNigeria a safiyar litinin.

Sanarwar ta kara da cewa gwamnan ya bayar da tabbacin ne bayan taron majalisar tsaron jihar da aka yi a ranar Lahadi tare da manyan jami’an tsaro, inda aka sake jaddada kudurin gwamnati na tabbatar da zaman lafiya a dukkan yankunan jihar.

Gwamnatin ta ce duk wani rahoto da ke yawo a kafafen sada zumunta na cewa akwai gagarumar barazanar tsaro a Kano, ba shi da tushe balle makama. Ta ce babu wani sahihin bayanan asiri da ke nuna akwai matsalar tsaro da ta taso ko ta gabatowa a jihar .

Sanarwar ta jaddada cewa gwamnati ba za ta lamunci yada bayanan ƙarya da nufin tayar da hankalin jama’a ba, tare da gargadin cewa irin wannan ɗabi’a na iya janyo hukunci daga hukumomi.

Gwamnatin ta bayyana cewa tana aiki kafaɗa da kafaɗa da hukumomin tsaro, tare da tabbatar da cewa jami’an tsaro sun kasance cikin shiri, kuma an tura su muhimman wurare, suna aiki ba dare ba rana domin tabbatar da zaman lafiya a Kano .

Sanarwar ta kara da cewa an sanya dukkan sassan Kano cikin tsauraran matakan sa ido, tare da ingantaccen tsarin tsaro da ke aiki yadda ya kamata.

Gwamnatin ta roki jama’a su kwantar da hankalinsu, su guji yada jita-jita a kafafen sada zumunta. Ta kuma yi gargaɗin cewa masu yada labaran ƙarya su daina, domin hakan na iya jawo wa mai yi hukunci.

Gwamna Abba Kabir Yusuf ya tabbatar da cewa gwamnati na kara inganta ayyukan leken asiri, haɗin kai tsakanin hukumomin tsaro, da kuma sabunta dabarun tsaro na zamani a fadin jihar Kano

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp