Home Labarai An ceto wasu daga cikin daliban da aka sace a makarantar Papiri...

An ceto wasu daga cikin daliban da aka sace a makarantar Papiri da ke jihar Neja

Gwamnatin tarayya ta tabbatar da ceto ɗalibai 100 daga cikin mutum 315 da ’yan bindiga suka sace a Makarantar St. Mary’s da ke Papiri, ƙaramar hukumar Agwara a Jihar Neja.

’Yan bindigar sun kai farmakin ne a ranar 21 ga Nuwamba, 2025, inda suka mamaye makarantar suka tafi da mutum 315 da suka haɗa ɗalibai 303 da malamai 12.

Rahotanni sun nuna cewa jami’an tsaro tare da mafarauta na yankin sun bazama cikin dazuzzukan da ke makwabtaka da Papiri domin neman waɗanda aka sace.

A rana ta farko bayan harin, yara 50 sun yi nasarar tserewa kuma suka koma hannun iyalansu lamarin da ya kawo addadin waɗanda suka rage a hannun ƴan bindigar zuwa mutum 265 kafin wannan sabon cigaba na ceto wasu daga cikinsu.

Gwamnatin Jihar dai ta bayyana cewa kafin aukuwar lamarin ta samu sahihan bayanan sirri game da yiwuwar tashin hankula a sassan Neja ta Arewa, saboda haka ta dakatar da ayyukan gine-gine tare da rufe makarantu masu kwana a yankunan da abin ya shafa.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp